Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Muna Alfahari Da Kai A Matsayinka Na Ɗanmu –Sakon Kungiyar CAN Ga Pantami

  Daga Auwal Adam Kungiyar kiristoci ta Nijeriya (CAN) reshen jihar Gombe ta kira ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani, Dr Isa Ali Pa...

 


Daga Auwal Adam

Kungiyar kiristoci ta Nijeriya (CAN) reshen jihar Gombe ta kira ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani, Dr Isa Ali Pantami da cewa dan ta ne mai albarka kamar yadda Jaridar SaharaReporters ta ruwaito.

CAN din ta bayyana hakan ne a cikin wata wasika wacce Sakataren kungiyar, Senior Apostle John Adedigba ya sanya hannu a madadin duk sauran ‘yan kungiyar inda ya kira Pantami da cewa dan su ne kuma suna alfahari da kasancewarsa dan su.

Kungiyar har wala yau ta taya Ministan Sadarwa, Isa Ali Pantami farin cikin samun karin matsayin zuwa daraja ta Farfesa a harkar tsaron yanar gizo.

CAN ta jihar Gombe ta kara da bayyana yadda Farfesa Isa Ali Pantami ya samu tarin nasarori daga hawansa kan mulki zuwa yanzu inda ta bayyana alfaharin da take yi da shi.


No comments