Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Mutum 4 Sun Mutu A Yayin Rikici Tsakanin Kungiyoyin Asiri A Binuwe

  Akalla mutum hudu ne suka rasa rayukansu a wani artabu tsakanin kungiyoyin asiri a karamar hukumar Gboko ta jihar Binuwe a ranar Laraba. W...

 


Akalla mutum hudu ne suka rasa rayukansu a wani artabu tsakanin kungiyoyin asiri a karamar hukumar Gboko ta jihar Binuwe a ranar Laraba.

Wani shaidar gani da ido, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa wasu kungiyoyin asiri guda biyu ne masu hamayya da juna suka gwabza fada da neman iko a yankin kuma hakan ya yi sanadiyyar mutuwar mutane hudun da ake kyautata zaton membobin kungiyoyin asiri ne.

Ta ce an kama mutane uku da ake zargi da hannu a kisan.

Ta kara da cewa ana ci gaba da bincike kuma za a gurfanar da wadanda aka samu da laifi bayan haka.


No comments