Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

'mutum 51 Aka Kashe A Cikin Kwana Biyu A Kudancin Kaduna'

  Rahotanni daga Kaduna na cewa mutum 51 suka rasa rayukansu a rikicin kwanaki biyu a yankunan Kudancin Kaduna. Akwai rahotannin da ke cewa ...

 


Rahotanni daga Kaduna na cewa mutum 51 suka rasa rayukansu a rikicin kwanaki biyu a yankunan Kudancin Kaduna.

Akwai rahotannin da ke cewa an rika kai hare-haren ramuwar gayya musamman a yankin Zangon Kataf, da suka yi sanadin salwantar rayukan fararen hula da ba su ji ba su gani ba.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da kungiyoyin kare hakkin bil'adama ke zargi kungiyar gwmanonin Arewa ta Northern Governors Forum da kin cewa komai kan kashe-kashen da ke faruwa a Kudancin Kaduna

Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa an kashe akalla mutun 48 a dan tsakanin nan biyo bayan hare haren 'yan bindiga a yankin.

No comments