Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Na Rufe Kofar Karbar Tuba Har Sai Na Karar Da ‘Yan Bindiga –Gwamna Matawalle

  Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana cewa; sakamakon lugudan wuta da jami’an tsaro ke yi wa ‘yan bindiga a dazukan jihar Zamfara, sun turo...

 


Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana cewa; sakamakon lugudan wuta da jami’an tsaro ke yi wa ‘yan bindiga a dazukan jihar Zamfara, sun turo wasu manyan mutane zuwa ga Gwamna Bello Matawalle suna tuba da neman sulhu. Gwamna Matawalle ya amsa masu da cewa, an kulle karbar tubar su, lugudan wuta yanzu aka fara.

Gwamna Matawalle ya bayyana haka bayan kammala sallar Juma’a a Masallacin Sabo dan Ashafa da ke Gusau.

Matawalle ya kara da cewa, a ranar Alhamis da ta gabata an turo Kwamitin Babba daga Garuruwan Mada, Ruwan Baura da Acha; “kan in zagaita wuta, sun tuba, na ce na rufe hanyar tuba ga Barayi ‘yan ta’adda , wallahi ba zan tsagaita ba, lokacin da muka nemi su tuba, su kaki. Kuma mun bi duk hanyar da ta dace a bi sun ki sai yanzu da suka ji wuta, don haka tsakaninmu da su sai mu hadu wajen Ubangijinmu”, Inji gwamna Matawalle kamar yadda Jaridar LEADERSHIP Hausa ta labarto.

Gwamna Matawalle ya kuma yi kira ga al’ummar jihar Zamfara da su ci gaba da bada hadin kai.

Kuma ya gargadi ‘yan siyasa da su daina ba mutane manyan Mashina masu amfani da kuloch, dan idan an ba su ne suke saidawa, sai barayi su saya su rika amfani da su a cewarsa.

“Don haka duk dan siyasa da muka kama yana bada irin wadannan Mashina lallai zamu hukun tashi”, inji Gwamna Matawalle.

 


No comments