Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Shugaba Buhari Ya Caccaki Amnesty International

  Shugabajn kasa Muhamamdu Buhari ya zargi Æ™ungiyar kare hakkin bil adama ta Amnesty da goyon-baya ta'addanci da ake aikatawa a Æ™asar. S...

 


Shugabajn kasa Muhamamdu Buhari ya zargi ƙungiyar kare hakkin bil adama ta Amnesty da goyon-baya ta'addanci da ake aikatawa a ƙasar.

Shugaban a wata sanarwa É—auke da sa hannun kakakinsa Malam Garba Shehu ya ce Amnesty wacce doka ba ta bata damar gudanar da ayyukanta a Nijeriya ba, a yanzu haka ta jefa siyasar cikin gida a lamuranta a cewarsa.

Shugaba Buhari ya zargi ofishin Amnesty na Nijeriya da neman farantawa wasu tsiraru da kira ga ƙungiyar ta binciki ayyukan jami'anta a Abuja.

Sanarwar dai ta ce Amnesty na kankamba a wasu batutuwan tsaron cikin gida da kare jagoran 'yan awaren IPOB wanda a dalilisan mutane da dama suka rasa rayukansu a Nijeriya.

Sannan ya ce ana amfani da Amnesty wajen rufe manyan laifuka, kuma wannan yanayi ne na Alla-wadai da ake gani a wata kasa ta Afirka.


No comments