Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Shugaban Kasar Iran Ya Ce Dole Ne A Hukunta Amurka Bisa Cin Zarafin Bil’adama A Afghanistan

  Daga Muhammad A. Dalhatu Madogara ta labarto cewa; shugaban kasar Iran, Ebrahim Raeisi ya ce dole ne a hukunta Amurka bisa take hakkin Bil...

 


Daga Muhammad A. Dalhatu


Madogara ta labarto cewa; shugaban kasar Iran, Ebrahim Raeisi ya ce dole ne a hukunta Amurka bisa take hakkin Bil’adama da ta yi a yakin da ta kaddamar a Afghanistan, wanda suka kashe dubban mata da kananan yara a yayin mamayar da suka yi.

Raesi ya bayyana hakan ne a yayin zaman da ya yi da majalisarsa, inda ya kara da cewa; abin da Amurka ta yi na tsawon shekaru 20 a Afghanistan ya nuna yadda ta gwanance a take hakkin Bil’adama da take ‘yancinsu, inda suka rika kashe mata da kananan yara tare da raunata wasu a yayin mamayarsu.

 “idan muka dauki adadin mata da kananan yaran da aka kashe, cin zarafinsu, da kuma raunata su a Afghanistan a tsawon shekaru 20, za mu ga irin mummunan bala’in da ya faru a kasar”, ya jaddada.  

Ya ce yakin da aka yi a Afghanistan yana tabbatar da cewa kasancewar sojojin Amurka a sassa daban -daban na duniya bai taba ba da gudummawa wajen kawo tsaro ba, sai dai ya lalata zaman lafiya, kwanciyar hankali da kuma tsaro.

No comments