Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

‘Shugaban Miyetti Allah Ya Mutu Ne A Hannun Masu Garkuwa’

  Kungiyar Miyetti ta masu kiwon shanu ta Nijeriya (MACBAN) ta sanar da mutuwar Alhaji Abubakar Abdullahi, wanda aka fi sani da Danbardi, ...

 


Kungiyar Miyetti ta masu kiwon shanu ta Nijeriya (MACBAN) ta sanar da mutuwar Alhaji Abubakar Abdullahi, wanda aka fi sani da Danbardi, Shugaban Kungiyar a Karamar Hukumar Lere ta Jihar Kaduna.

Kungiyar ta sanar da hakan ne a cikin wata sanarwa da Sakataren ta na kasa, Othman Ngelzarma, ya bai wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) a ranar Asabar, a Abuja, yana mai cewa masu garkuwa da mutane sun kashe Marigayin, mai shekaru 58 a ranar Juma’a.

Sanarwar ta ce "Mutuwar Abubakar ta kawo adadin jami'an MACBAN biyar da 'yan bindiga, masu garkuwa da mutane ko barayin shanu suka kashe a wannan shekarar a fadin kasar".

Ngelzarma ya bayyana cewa an tsinci gawar Abdullahi a bakin hanya a ranar Juma’a, bayan an sace shi daga gidansa dake Lere a ranar 16 ga Satumba kuma bayan an biya kudin fansa.

“An yi garkuwa da Alhaji Abubakar, mai shekaru 58 a ranar 16 ga Satumba kuma bayan ya biya kudin fansa aka tsinci gawarsa a bakin hanya a ranar Juma’a, 17 ga Satumba a wajen garin Lere.

"Yayin da muke jajantawa iyalan mamacin, MACBAN reshen jihar Kaduna, muna kira ga hukumomin tsaro da su binciki wannan da sauran miyagun ayyuka da dama a fadin kasar tare da gurfanar da masu laifin a gaban kuliya," in ji Ngelzarma.

Sakataren MACBAN na kasa ya yi tir da karuwar rashin tsaro da membobin kungiyar ke fuskanta a duk fadin kasar, ko dai daga masu garkuwa da mutane ko ‘yan bindiga.

Ya ce: “Kalubalen yana sa ku san ba zai yiwu membobinmu su gudanar da harkokinsu cikin kwanciyar hankali ba. Wannan wani bangare ne da ke sanya tsadar dabbobin da kayayyakin dabbobin.

“Idan rashin tsaron ya ci gaba, yana iya durkusar da harkar kiwon dabbobi a kasar nan.

"Don haka muna kira ga Gwamnatin Tarayya da ta tabbatar da cewa an aiwatar da sabbin manufofin da aka tsara domin inganta harkar kiwo", in ji shi.

No comments