Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Sojan Da Aka Yi Garkuwa Da Shi A NDA Ya Samu ‘Yanci

  Daga Muhammad Haruna  Manjo CL Datong, wanda ‘yan bindiga suka yi garkuwa da shi bayan da suka kai hari makarantar horas da sojoji ta ND...

 


Daga Muhammad Haruna 

Manjo CL Datong, wanda ‘yan bindiga suka yi garkuwa da shi bayan da suka kai hari makarantar horas da sojoji ta NDA dake Kaduna a watan da ya gataba, ya samu ‘yanci a karshe.

A yayin harin na ‘yan bindiga a ranar 24 ga watan Agustan 2021, an kashe jami’an soji biyu.

A daren Juma’a ne, mataimakin Daraktan Hulda da jama’a na soji na Division 1, Kanal Ezindu Idimah, shi ne ya bayyana cewa rundunarsu ce ta yi nasarar ‘yanto Datong.

Ya ce samamen da suka kai wajen ‘yanto sojan ya sanya sun tarwatsa sansanonin ‘yan bindiga da dama a Afaka zuwa Birnin Gwari dake jihar.

Ya ce sun kashe ‘yan bindiga da dama a yayin samamen, musamman samamen da suka kai a daren ranar 17 ga watan Satumban 2021.

Ya ci gaba da cewa rundujar sojin tare da hadin guiwar sojin sama, hukumar tsaro ta DSS, da sauran hukumomin tsaro, sun kai samamen ne cikin hanzari inda suka gudanar a kafatanin yankin Afaka domin ‘yanto jami’in sojan bayan da shugaban Hafsan sojojin Nijeriya ya bada umurni.

Sojojin sun isa sansanin da ake zargi shi ne wurin da ake tsare da Manjo CL Datong. A sansanin, sojojin sun yi musayar wuta tare da 'yan bindigar inda suka sha karfinsu.

 “A cikin haka, sojojin sun galabar nasarar kubutar da jami’in da aka sace. Duk da haka, jami’in ya samu rauni kadan amma an yi masa magani a wani asibiti kuma an mika shi ga NDA don ci gaba da daukar mataki, ”inji shi.

Ya yaba da kokarin NAF, DSS, 'Yan sandan Nijeriya da "yan Najeriya masu kishin kasa" saboda tallafin da aka su wanda ya ce taimaka wajen nasarar aikin da suka yi.

Ya ce su za su ci gaba har sai sun kamo ko kuma sun kashe maharan da suka kashe jami’ai biyu (2) a cikin NDA.


No comments