Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Taliban Ta Sanar Da Nadin Manyan Jami'an Sabuwar Gwamnatin Afghanistan

  Kungiyar Taliban ta sanar da kafa sabuwar gwamnatin rikon kwarya a Afghanistan, wata guda bayan kwace iko da kasar daidai lokacin dandazon...

 


Kungiyar Taliban ta sanar da kafa sabuwar gwamnatin rikon kwarya a Afghanistan, wata guda bayan kwace iko da kasar daidai lokacin dandazon matan ke ci gaba da zanga-zangar neman ‘yanci da kuma shigar da su harkokin tafiyar da gwamnati.

A wani taron manema labarai da kakakin kungiyar Zabihullah Mujahid ya gabatar a yau Talata, ya sanar da cewa dukkanin mukaman da za a nada yanzu za su kasance na rikon kwarya inda ya bayyana Mullah Mohammad Hasan Akhund a matsayin shugaban sabuwar gwamnatin yayin da guda cikin ma’assasan kungiyar ta Taliban Abdul Ghani Baradar zai zama mataimaki.

Haka zalika Mujahid ya sanar da sunan Mullah Yaqub, dan Marigayi Mullah Omar tsohon shugaban majalisar koli kuma guda cikin wadanda suka kafa kungiyar a matsayin ministan tsaro sai kuma Sirajuddin Haqqani a matsayin ministan cikin gida wanda shi ne tsohon mataimakin shugaban kungiyar ta Taliban.

Haka zalika nade-naden na Taliban ya sanar da sunan Amir Khan Muttaqi babban mai shiga Tsakani na kungiyar a Doha matsayin ministan harkokin waje.

A cewar Mujahid Taliban za ta yi kokarin shigar da wasu mutane daga waje cikin kowanne sashe na kasar don ba su mabanbantan mukamai.

 


No comments