Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Yadda Mafarauta Suka Kashe 'Yan Bindiga 47 A Jihar Neja

  Mafarautar gargajiya sun yi nasarar kashe ‘yan bindiga 47 da suka hana mutanen Shiroro dake Jihar Neja zaman lafiya na dogon lokaci. Jar...

 


Mafarautar gargajiya sun yi nasarar kashe ‘yan bindiga 47 da suka hana mutanen Shiroro dake Jihar Neja zaman lafiya na dogon lokaci.

Jaridar PRNigeria da ake wallafawa a Nijeriya ta ce mafarautar sun kaddamar da harin ne a Magami dake tsakanin kananan hukumomin Shiroro da Rafi inda suka hallaka ‘Yan bindigar a ranar larabar da ta gabata.

Majiyar jaridar tace ‘yan bindigar sun dade suna amfani da ‘yankin dake kusa da gabar ruwa wajen fakewa suna kai wa jama’a hare hare a yankunan jihar.

Jaridar ta ce wani jami’in ‘Yan sanda ya tabbatar mata cewar bayan kashe 47 daga cikin su, wasu da dama sun tsere da harbin bindiga a jikin su.

Jihar Neja na daya daga cikin jihohin da ‘Yan bindiga suka hana jama’a sakewa, inda suke kai hari garuruwa suna kashe mutane da kuma kwashe wasu domin karbar kudin fansa.

Rfi Hausa ta labarto cewa; ko a makon jiya sanda ‘Yan bindigar suka karbi kudin fansa kafin sakin daliban Islamiyar Tegina wadanda suka kwashe kwanaki 88 a hannun su.

Gwamnan Jihar Abubakar Sani Bello ya kafa wata rundunar ‘Yan Sakai dake samun tallafin sojoji da ‘Yan Sanda domin taimakawa jami’an tsaron tabbatar da zaman lafiya a jihar.

Bello ya ce ‘Yan bindigar sun jefa jama’ar sa cikin halin kakanikayi wajen hana ‘yayan su zuwa makaranta da hana jama’a tafiye tafiye da gudanar da harkokin noma, amma kuma ba za su bada kai bori ya hau ba.

 


No comments