Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum 34 A Kaduna

  ‘Yan bindiga sun hallaka mutum akalla 34 tare da raunata wasu da dama a wani hari da suka kai a kauyen Madamai da ke karamar hukumar Kaura...

 


‘Yan bindiga sun hallaka mutum akalla 34 tare da raunata wasu da dama a wani hari da suka kai a kauyen Madamai da ke karamar hukumar Kaura a Kudancin jahar Kaduna.

Daruruwa sun tsere daga gidajensu bayan wani harin 'yan bindiga da ya janyo asarar rayuka akalla 34, maharan sun kona gidaje bayan kashe-kashen jama'a a kauyen Madamai da ke karamar hukumar Kaura na yankin kudancin jahar Kadunan. 

Mista Samuel Aruwan wanda shi ne Kwamishinan harkokin cikin gida da tsaron Jihar ta Kaduna ya tabbatar da aukuwar harin a wata sanarwar da ya fitar a yau din nan.

An soma tuhumar wasu da ake zargin nada hannu a harin inji Aruwan, har wa yau a jiya Lahadin, wasu 'yan bindiga sun kai hari kan masu ibada a wani coci da ke Kachia a jahar ta Kaduna inda suka kashe mutum guda da raunata wasu da dama.

Rahotanni na cewa jama'a na tserewa saboda fargabar ramuwar gayya, sai dai an jibge jami'an tsaro a yayin da gwamnan jihar Nasiru El-Rufai, ya umurci Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar, da ta gaggauta kai ma wadanda harin ya rutsa da su kayayyakin agaji.

Daruruwan Jama'a ne yanzu haka ke gudun hijira a yankin Kudancin Kaduna sakamakon karuwar hare-haren 'yan bindiga da rigingimun masu nasaba da addinai tare da kabilanci

 


No comments