Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

'Yan Bindiga Sun Hallaka 'Yan Sanda Da Sojojin Nijeriya 12 A Jihar Zamfara

  Wasu 'yan bindiga sun kashe jami'an tsaron Nijeriya 12 a wani hari da suka kai karshen makon da ya gabata kan wani sansanin soji...

 


Wasu 'yan bindiga sun kashe jami'an tsaron Nijeriya 12 a wani hari da suka kai karshen makon da ya gabata kan wani sansanin soji a jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin kasar, kana suka sace makamai da kona gine -gine, in ji majiyoyin tsaro.

Ba a dai bayyana ko su wanene suka kai samamen na ranar Asabar a Mutumji ba, amma sojoji na ci gaba da luguden wuta kan 'yan fashin daji wadanda ake zargi da laifin garkuwa da mutane.

An kuma katse hanyoyin sadarwa a Zamfara da wasu sassan makwabciyar jihar Katsina a kokarin hana yan fashin sakat.

Wata majiya ta shaida wa kamfanin dillacin labaran Faransa AFP cewa “Maharan sun kutsa cikin sansanin ne da misalin karfe 10:30 na safe kuma suka fafata da sojojin a wani mummunan artabu,” in ji wata majiyar tsaro.

"Sun fatattaki sojojin sun kashe 12 daga cikinsu. da suka hadar da sojojin ruwa tara, da soja da 'yan sanda biyu."

Sansanin da ke Mutumji, gundumar Dansadau, mai tazarar kilomita 80 daga Gusau babban birnin jihar, muhimmin wuri ne da sojojin kasar ke amfani da shi wajen shirya dabaru da tattara bayanai a yakin da suke yi da yan bindiga a jihar.

Zuwa yanzu dai rundunar sojin Nijeriya bata ce komai dangane da batun ba tukunna.


-BBC Hausa

No comments