Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

‘Yan Bindiga Sun Kashe Magidanci A Jihar Zamfara

  Marigayi Sanusi Bala Daga Wakilinmu MADOGARA ta labarto cewa; ‘yan bindiga a jihar Zamfara sun kashe wani mutum mai suna Sanusi Bala Shi...

 

Marigayi Sanusi Bala

Daga Wakilinmu

MADOGARA ta labarto cewa; ‘yan bindiga a jihar Zamfara sun kashe wani mutum mai suna Sanusi Bala Shinkafi. Lamarin ya faru ne a yau Laraba, a inda ‘yan bindigar suka yi masa kisan gilla a titin Shinkafi zuwa Kaura Namoda.

Falalu Hassan, ya wallafa cewa; “Innalillahi wa’inna Ilaihi Raji'un. Yanzu haka ina Sokoto nake samun labarin bakin ciki na kashe dan uwanmu Sanusi Bala Shinkafi. ‘Yan bindiga ne suka kashe shi a hanyar Shinkafi zuwa Kaura Namoda. Shi babban Yaya ne ga abokina, Alhaji Ahmad Bala Maths, shugaban Kamfanin Mass communication Nigeria Enterprises”, ya tabbatar.

Ya kara da cewa; “Marigayi Sanusi Bala  ba kawai dan uwa bane, Uba ne da dukkanin ma’ana. Allah ya jikansa da Rahama ya karbi shahadarsa, ya isar mana ga jininsa da aka shekar bisa zalunci”, inji shi.

Kazalika shima dan uwan Marigayin ya tabbatar da kashe dan uwan na shi a shafinsa na Facebook, inda ya labarta cewa; “Innalillahi wa’inna Ilaihi Raji'un. ‘Yan bindiga sun kashe dan uwana Sanusi Bala Shinkafi a titin Moriki. Muna rokon Allah ya karbi shahadar shi ya gafarta masa kurakurensa. Wallahi mun yi rashin Uba garkuwan gidanmu Sadauki”, ya nusasshe.

Jihar Zamfara dai na daya daga cikin jihohin Arewa maso yamma da ‘yan bindiga suka addabe ta da kashe-kashe da kuma garkuwa da jama’a. Wanda wannan dalilin ya sanya gwamnatin jihar ta dauke matakin katse hanyoyin sadarwa baki daya.


No comments