Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

‘Yan Bindiga Sun Kashe Soja Da Garkuwa Da Matar Aure Da ‘Ya’yanta 2 A Zariya

  Daga Ammar Muhammad   ‘Yan bindiga sun kashe soja daya tare da garkuwa da wata matar aure da ‘ya’yanta biyu a Unguwar Milgoma dake kus...

 


Daga Ammar Muhammad

 ‘Yan bindiga sun kashe soja daya tare da garkuwa da wata matar aure da ‘ya’yanta biyu a Unguwar Milgoma dake kusa da Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello dake Shika a Zariya ta jihar Kaduna.

Wakilinmu ya labarto mana cewa lamarin ya auku ne da misalin karfe 9 na daren ranar Litinin kamar yadda mazauna Unguwar suka tabbatar mana.

Majiyarmu ta labarta mana cewa sojan da ‘yan bindiga suka raunata bayan sun yi musayar wuta a tsakaninsu a lokacin da sojojin suka yi yunkurin dakile harin ‘yan bindiga ya cika ne a wani asibiti da ba a bayyana sunansa ba ya zuwa hada rahoton nan.

Majiyarmu ta labarta mana cewa ‘yan bindigar sun zo da yawan gaske da adadin ya kusan kai wa 40 dauke da muggan makamai inda suka yi harbin kan mai uwa da wabi bayan da suka farmaki al’ummar Unguwar.

Sai dai gamayyar Jami’an tsaron sa kai na KADVIS (Kaduna State Vigilance Service) da sojoji da ‘yan sanda sun yi hanzarin kawo wa Unguwar dauki bayan da suka amsa kiran gaggawa da aka yi musu, inda majiyarmu ta ce bayan da ‘yan bindigar suka lura da isowar Hukumomin tsaron ne suka bude musu wuta inda a nan ne suka yi musayar wuta da ya yi sanadin rasuwar soja daya.

Babu tabbataccen rahoto kan ko an jikkata ‘yan bindiga ya zuwa hada rahoton nan.

Malam Haruna Shika, wani mazaunin Unguwar, ya shaidawa Daily Trust cewa hukumomin tsaro sun yi nasarar kwato yara shida da aka yi garkuwa da su a Kasuwan [a’a a Zariya.

Laftanar Joy Abah, Mukaddashiyar  Daraktan hulda da jama’a na sojoji na Barikin sojoji na Depot Zariya ta ce ba a tabbatar mata da mutuwar sojan ba tukunna ya zuwa hada rahoton nan.

 

No comments