Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

‘Yan Gudun Hijira 450 Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Maida Su Garuruwan Su

Kwamishiniyar Ma'aikatar Jinkai, Hajiya Faika Ahmad   Daga Hussaini Ibrahim, Gusau Gwamnatin jihar Zamfara karkashin jagorancin Gwamna...

Kwamishiniyar Ma'aikatar Jinkai, Hajiya Faika Ahmad 

Daga Hussaini Ibrahim, Gusau

Gwamnatin jihar Zamfara karkashin jagorancin Gwamna Bello Muhammad Matawalle ta maida 'yan gudun Hijira 450  garuruwan su sakamakon harin 'yan ta'adda.

Kwamishiniyar Ma'aikatar Jinkai, Hajiya Faika Ahmad ce ta bayyana haka a lokacin da ake kwashe  ‘yan gudun Hijira da ke Zaune a cikin garin Gusau, babban birnin jihar.

Hajiya Faika Ahmad ta bayyana cewa, wadannan  ‘yan gudun Hijira daga Kananan hukumomin Kauran Namoda, Zurmi, Shinkafi, Birnin Magani da Gusau, an maida su garuruwan su ta hannun Sarakuna iyayen kasa tare da rakiyar jami'an tsaro. “kuma mun bai wa ‘yan gudun Hijira tallafin kayan masarufi da kudi da zai ba su damar zama a cikin garuruwan na s”, inji Kwamishiniyar.

Kuma ta tabbatar da cewa, Ma'aikatar ta na iyaka kokarin ta wajen tallafawa mata da kananan Yara da suka rasa abinci da muhalli domin ganin sun samu saukin rayuwa.

Kuma Gwamnati jihar, karkashin jagorancin gwamna Matawalle tare da Gwamnatin tarayya na iyaka kokarinsu su wajrn ganin sun tallafawa al'umma da annoba ta shafa a fadin jihar ta Zamfara.


No comments