Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

'Yan Nijeriya Miliyan 27 Da Rabi Basa Samun Naira Dubu 100 A Shekara - SERAP

    Wani bincike da kungiyar SERAP dake sanya ido akan tattalin arziki da kuma tabbatar da jagoranci na gaskiya a Najeriya ta fitar yace aka...

 

 

Wani bincike da kungiyar SERAP dake sanya ido akan tattalin arziki da kuma tabbatar da jagoranci na gaskiya a Najeriya ta fitar yace akalla Yan Najeriya miliyan 27 da rabi ne basa iya samun naira dubu 100 a shekara guda.

Rahotan da kungiyar ta gabatar a Lagos yace wannan adadin da ya kai kusan kashi 49 na al’ummar kasar kuma ya dada fito da tsananin talaucin da ya addabi jama’ar Najeriya duk da arzikin Allah Ya wadata kasar da shi.

Rahotan da aka yiwa lakabi da ‘Yadda cin hanci da rashawa suka yiwa harkar bada ilimi da kula da lafiya da samar da ruwan sha illa’, ya mayar da hankali ne a shiyoyi 6 na Najeriya domin sanin halin da jama’a suke ciki.

Yayin gabatar da rahotan, Elijah Okebukola, wani babban mai bincike a Cibiyar horar da jami’an yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya dake karkashin Hukumar ICPC yace kashi 28 na Yan Najeriya ko kuma mutane miliyan 15 da rabi ke rayuwa tsakanin naira dubu 200 zuwa kasa da dubu 100 a shekara, yayin da kashi kusan 11 ke samun tsakanin naira dubu 201 a shekara zuwa naira dubu 300, sai kuma kashi 12 da rabi dake samun sama da naira dubu 300 a shekara.

Rahotan yace akasarin wadanda suka fi jin radadin halin kuncin talaucin da ya addabi jama’ar kasar talakawa ne wadanda ake ci da gumin su ta irin makudan kudaden da ake warewa domin kula da lafiyar su da samarwa ‘yayan su ilimi da kuma tsaftacaccen ruwan sha.

Rahotan yace jihohin Najeriya basu da wata shaidar bayanan dake nuna yadda suke taimakawa jama’a wajen yaki da talauci a hukumance, ko kuma inganta rayuwar su ta bangaren kula da lafiyar su da kuma samar musu da ilimi.

Okebukola yace koda an samu daidaikun jihohin dake kokarin kamanta irin wadannan ayyuka mutanen su basu ma san ana yi ba.

Rahotan yace daga cikin kashi 79 na mutanen Najeriya dake zama cikin talauci sama da miliyan 44 sun dogara ne da shan ruwan rijiya ko kuma rijiyar birtsatsai, yayin da kashi 34 ko kuma miliyan 19 basu damu da zuwa asibitocin gwamnati domin samun magani ba.

Rahotan yace sama da kashi 5 ko mutane kusan miliyan 3 da suka je asibitin gwamnati an hana su magunguna ko kuma kular da ta dace.

Rahotan ya kara da cewar sama da kashi 4 ko kuma mutane miliyan 2 da rabi basu taba samun abinda ake kira tallafin da gwamnati ke ikrarin rabawa marasa galihu ba.

Kungiyar SERAP tace duk da tabarbarewar harkar bada ilimi a Najeriya wajen rashin kayan aiki da kuma gine ginen azuzuwa, talakawa na tunanin samun ingantaccen ilimi a makarantun gwamnati.

Jaridar Premium Times tace rahotan ya bukaci sake fasalin kundin tsarin mulkin Najeriya da ake amfani da shi yanzu domin sanya ‘yancin jama’a na samun ilimi da kula da lafiyar su da kuma tsaftacaccen ruwan sha a matsayin hakkokin jama’ar kasa.

-RFI Hausa 

No comments