Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Musulmai Sun Yi Raddi Ga Sheikh Gumi Bayan Sukar Da Ya Yi A kan Mauludi

Dan Bala Jarida Radio ta labarto cewa; Musulman Najeriya sun mamaye shafin Facebook na Dr. Ahmad Gumi, shahararren mai fafutukar kare ha...


Dan Bala

Jarida Radio ta labarto cewa; Musulman Najeriya sun mamaye shafin Facebook na Dr. Ahmad Gumi, shahararren mai fafutukar kare hakkin ‘yan fashin daji bayan yayi suka ga maulidi a shafin a daidai lokacin da musulman suke  tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad SAWA.

A kowace shekara a cikin watan Rabi’ul Awwal, Musulmin duniya suna tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad ta hanyar karanta AlÆ™ur’ani mai girma, Æ™asidun yabo ya Annabi da karanta tarihin rayuwar sa.

Shafin Dr. Gumi na Facebook ya samu sharhi sama da 600 har zuwa lokacin nan a tare da cewa suka yayi akan maulidin, amma da yawan su suna rubuta "Happy Maulud,"  duk da sun karanta sukar da yayi. 

Karantarwar Dr Gumi tana fuskantar tsaiko da rashin tasiri akan mutane bayan ya karkatar da hankalin sa daga taimakon waɗanda rikicin yan fashin daji ya rutsa da su a arewa maso yammacin Najeriya zuwa neman haƙƙin masu aikata laifin.

No comments