Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Rusau A Zariya: An Zargi Sojoji Da Kashe Mutum Bakwai

  Shugaban Sojin Nijeriya, Laftanar Janar Farouk Yahaya Daga Wakilinmu A ranar Talatar 5 ga watan Oktoban 2021 ne, gwamnatin Jihar Kaduna ta...

 

Shugaban Sojin Nijeriya, Laftanar Janar Farouk Yahaya


Daga Wakilinmu

A ranar Talatar 5 ga watan Oktoban 2021 ne, gwamnatin Jihar Kaduna ta fara rusa daruruwan gidaje da sauran gine-ginen gidaje dake Unguwar Graceland a bayan Kwalejin Fasaha ta Koyar da Jirgin Sama (NCAT) dake Samarun Zariya kamar yadda MADOGARA ta labarto.


Wani bangare na gidajen da aka rushe a Unguwar Graceland. 


Wakilinmu da ya halarci Unguwar kafin a kai ga rushe gidajen ya ga mazauna da yawa suna ta kuka a yayin da suke ficewa cikin gaggawa daga gidajensu da abin da ya rage na kadarorinsu daga baraguzan gidaje da aka rushe musu.Sai dai kafin a kai ga rushewa, wadansu ba’adin mutanen Unguwar sun yi sa’ar samun damar kwashe wadansu kayayyakinsu masu muhimmanci kafin hukumar raya birane ta jihar Kaduna (KASUPDA) ta kai kayayyakinta ta fara rushe gidajen dake wurin.

Bayan jimami da kukan da ya biyo bayan rushe muhallin, akwai kuma zargin kashe wadansu masu gidajen da ake zargin sojoji da aka tura wurin rusa wurin sun aikata, duk da cewa rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta musanta batun kashe-kashen da kuma harbin da sojoji suka yi ba bisa ka’ida ba.

Kazalika, bayanai sun nuna cewa sama da shekaru 10, batun mallakar fili a wurin, inda aka gina gidajen yana gaban shari'a tsakanin al'ummomi muhallin da Kwalejin koyon tukin jirgin Sama (NCAT).

Mazaunin Unguwar ya shaidawa majiyarmu cewa; tun ranar Asabar; “mutane da dama suka fara barin Unguwar inda suka rika kwashe muhimman kayayyakinsu domin kaucewa lalata musu shi”, ya tabbatar.

Wakilinmu da ya ziyarci a Unguwar da safiyar ranar Larabar 13 ga watan Oktoban 2021, ya iske daruruwan gidaje a rushe a bayan Kwalejin NCAT din, wanda ganau suka tabbatar mana da cewa KASUPDA ce ta rushe su a makon da ya gabata na 5 ga Oktoban 2021.

Wasu mazauna yankin, wadanda suka yi magana da manema labarai sun yi kira ga gwamnati "da ta nuna jinkai ta yi la’akari da halin da muke ciki kuma ta taimaka mana", inji su.

Mazauna Unguwar sun ce sun mallaki filin ne bisa doka tare da mallakar duk wasu takardu na doka daga gwamnati.

Sai dai lokacin da majiyarmu ta tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Mohammed Jalige, kan batun kashe wasu mazauna Unguwar da ake zargin sojoji da yi a yayin Rusau din, ya ce har yanzu bai samu rahoto ba kan zargin harbin da sojoji suka yi da kuma kashe wasu mazauna Unguwar.

Jalige ya ce, "ba ni 'yan mintoci kadan domin na binciki gaskiyar lamarin kuma zan dawo gare ku," in ji Jalige. Sai dai har ya zuwa hada rahoton nan, bai bayyana gaskiyar lamarin ba.

Kungiyar masu fafutikar kare hakkin Dan Adam, wato Kungiyar Marubutan Hakkokin Dan Adam ta Nijeriya (HURIWA), ta yi Allah wadai da abin da ta kira ‘kisan gilla’ da aka yi wa wasu masu gida bakwai a Unguwar Graceland kusa da Kwalejin koyon tukin jirgin Sama dake Zariya.

Kungiyar ta kare hakkin Dan Adam, a cikin wata sanarwa daga Shugabanta na kasa, Kwamared Emmanuel Onwubiko, da Daraktan yada labarai na kasa, Miss Zainab Yusuf, sun ce gwamnatin jihar Kaduna ta aikata manyan laifuka akan bil adama ta hanyar amfani da karfin soji wajen fatattakar 'yan kasa ba bisa ka'ida ba.

HURIWA suma sun yi zargin cewa sojoji sun kashe mutum bakwai a yayin rushe gidajen Unguwar, inda suka ce; "Muna da tabbaci cewa ya zuwa yanzu mutum bakwai ne sojojin da suka yi rakiyar jami’an rushe-rushen gwamnatin Kaduna suka kashe”, inji su, inda suka yi ikirarin cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya ba da umarnin yin hakan domin bai wa kwalejin jirgin sama damar fadada wuraren horas da ita a kusa da su.

Sun nuna mamakinsu bisa dokar da shugaban kasar ya yi amfani da shi wajen “take hakkin ‘yan kasa, wasu daga cikinsu sun yi aiki tukuru domin gina tattalin arzikin jihar Kaduna ”.

 “An jawo hankalinmu ga irin wahalar da wani Likita ya sha, wanda aka ruguza gidansa a Zariya da safiyar jiya (Talata) inda aka yi watsi da shi bayan ya roki Gwamnatin Jihar Kaduna cewa gidan shi ne duk abin da ya mallaka a rayuwar nan”, inji HURIWA.

Ta ci gaba da cewa; "an azabtar da shi ta jiki, ta kwakwalwa da zuciya, kuma an rushe kadarorinsa ba tare da la'akari da shekarunsa ba da kuma cewa ya yi ritaya a matsayin ma'aikacin gwamnati bayan ya yi kusan shekaru 40 na rayuwarsa mai albarka”.

 “Matakin da gwamnatin jihar Kaduna ta dauka haramtacce ne, ya sabawa kundin tsarin mulki, kisan kai ne, cin mutunci ne, abin kyama ne kuma abin zargi ne. Muna kira ga Majalisar [inkin Duniya, Tarayyar Turai, Amnesty International, Human Rights Watch na New York da duk mutanen da ke da niyyar yin Allah wadai da wadannan munanan laifuffukan da Sojojin Nijeriya ke aikatawa tare da neman a yi adalci ga wadanda aka kashe ba bisa ka’ida ba”, HURIWA ta jaddada.

Ta kuma kara da cewa; "Muna kira da a kama tare da gurfanar da dukkan jami'an tsaro da kwamandojin Sojojin da suka ba da umarnin kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba wanda laifinsu kawai shi ne neman amfani da karfinsu wajen kare kadarorinsu".

Kungiyar ta jaddada cewa ta yanke shawarar rubutawa Majalisar Dinkin Duniya, Kungiyar Tarayyar Turai da Kungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), domin kai karar gwamnatin Kaduna da Gwamnatin Tarayya kan kisan gilla da aka yi wa 'yan kasa a Zariya.

 

No comments