Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Sanata Ahmed Lawan Ya Taya Musulmin Najeriya Murnar Zagayowar Ranar Maulidi

Shugaban majalisar dattijan Najeriya, Ahmad Lawan ya taya al'ummar Musulmi murnar zagayowar ranar Maulidi a wata sanarwa da ya fitar. ...


Shugaban majalisar dattijan Najeriya, Ahmad Lawan ya taya al'ummar Musulmi murnar zagayowar ranar Maulidi a wata sanarwa da ya fitar.

BBC ta labarto cewa Ahmed Lawan ya ce ranar Maulidi rana ce da ya kamata Musulmi da sauran mabiya wasu addinan su tuna da alfanun zaman lafiya da girmama juna kamar yadda Annabi Muhammadu Salallahu Alaihi Wasallamya koya mana tsawon rayuwarsa ta tsoron Allah.

Ya ce yin hakan na da matukar amfani a yanzu da ake tsananin bukatar waɗannan halaye nasa don kawo waraka a ƙasarmu tare da karfafa danƙon zumunci a matsayinmu na mutane masu imani kuma ƴan Najeriya.

"Gwamnatin Najeriya da Majalisar dokoki za su ci gaba da yin aiki sosai don samar da yanayi mai kyau na zaman lafiya da fahimtar juna da ci gaba Najeriya," a cewarsa.

Ya kuma bukaci yan Najeriya su ci gaba da addu'a da tallafa wa hukumomin tsaro a koƙarinsu na kare yan kasar.

No comments