Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 10 Da Kona Gidaje A Filato

Rahotanni daga Filato na cewa an kashe aƙalla mutum 10 tare da ƙone gidaje a wani hari da ƴan bindiga da ba a tantance ba suka k...



Rahotanni daga Filato na cewa an kashe aƙalla mutum 10 tare da ƙone gidaje a wani hari da ƴan bindiga da ba a tantance ba suka kai a Te’egbea ƙaramar hukumar Bassa.

Kwamishinan Watsa Labarai na jihar, Mr Dan Manjang, wanda ya tabbatar wa da BBC da faruwan lamarin ya ce zuwa yanzu ba a tantance adadin hasarar rayuka da dukiya ba.

Wasu rahotanni sun ce an kai harin ne a cikin dare zuwa wayewar safiyar Juma’a inda ƴan bindigar suka buɗe wuta tare da cinna wa gidaje wuta.

No comments