Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Cikin Kwana Biyu Kacal 'Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum 53 A Jihar Sakkwato

  Mutum akalla 57 ‘yan bindigan Daji suka kashe a jihar Sakkwato a cikin kwanaki biyu da suka gabata. Bayanai na nuna da cewa a karamar Huku...

 


Mutum akalla 57 ‘yan bindigan Daji suka kashe a jihar Sakkwato a cikin kwanaki biyu da suka gabata.

Bayanai na nuna da cewa a karamar Hukumar Goronyo mutum  43 aka kashe sai kuma mutum 14 a yankunan Sabon Birni duk dai a Jihar ta Sakkwato.

Harin na zuwa ne jim kadan bayan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umarci a kara tura sojoji yankin domin a murkushe ‘yan bindigar dajin da suka hana sukuni a yankin.

Wani mazaunin yankin wanda ya gaskata harin ya bayyana cewa ‘yan bindigar dajin sun mamaye kauyuka dake yankin Unguwar Lalle tun daren Talata inda suke ta ayyukan ta’addanci.

Gwamnan Jihar Sakkwato Aminu Tambuwal ya fadi cewa suna ci gaba da kokarin kawo karshen hare-haren.

Kwamishinan ‘yan Sandan jihar Kamaludeen Okunlola ya gaskata hare-haren da aka kai inda ya ce suna iyakacin kokarin kama ‘yan bindigar kamar yadda majiyarmu ta labarto mana.

No comments