Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Har Yanzu Ba A San Adadin Mutanen Da Ƴan Bindiga Suka Sace Ba A Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

  Rahotanni sun bayyana cewa har yanzu ba a san adadin mutanen da ke hannun ƴan bindiga ba tun bayan harin da aka kai kan hanyar...


 Rahotanni sun bayyana cewa har yanzu ba a san adadin mutanen da ke hannun ƴan bindiga ba tun bayan harin da aka kai kan hanyar Kaduna zuwa Abuja ba a ranar Lahadi.

A jiya Litinin ne gwamnatin Kaduna da rundunar ƴan sandan jihar ta ce ta ceto mutum 11 bayan musayar wuta da ƴan sanda da sojoji suka yi da ƴan bindiga.

Sai dai hukumomin har yanzu ba su tantance yawan mutanen da aka sace ba. Sai dai Jami’an sun ce sun samu motocin matafiya da dama ba kowa a cikinsu, wasu a cikin daji wasu kuma a gefen hanya.

Harin na hanyar Kaduna zuwa Abuja ya yi ajalin tsohon ɗan takarar gwamnan Zamfara Alhaji Sagir Hamidu.


Karanta wannan; 'Yan Bindiga Sun Kashe Tsohon Dan Takarar Gwamna a Zamfara A Hanyar Abuja Zuwa Kaduna

Karanta wannan; An Yi Jana'izar Dan Siyasar Zamfara Da 'Yan Bindiga Suka Kashe A Hanyar Abuja


No comments