Marigayi Alhaji Musa Daga Muhammad Farouk Wadansu da ake zargin masu kisan kai ne sun yi wa wani magidanci da ...
Marigayi Alhaji Musa
Daga Muhammad Farouk
Wadansu da ake zargin masu kisan kai ne sun yi wa wani magidanci da matarsa kisan gilla a karamar Hukumar Malam Madori ta jihar Jigawa kamar yadda majiyarmu ta labarto.
Ma'auratan wanda aka bayyana da Alhaji Musa da Hajiya Adama an kashe su a daren ranar Asabar da misalin karfe 2:30.
Kakakin 'yan sandan jihar, ASP Lawan Shiisu, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa wadanda ake zargi da kisan kan sun farmaki gidan Marigayin ne a Kauyen Kebberi inda suka harbe su dukkansu.
Kakakin ya ci gaba da cewa; wadanda ake zargi da kisan kan ba su dauki komai daga wanda suka kashe ba, wanda yake Manaja ne a Kamfanin 'Three Brothers Rice Mill' a Hadeija.
"A ranar 13 ga watan Nuwamba, wadansu da 'yan ta'adda suka haura gidan wani mai suna Alhaji Musa, Manaja a Kamfanin 'Three Brothers Rice Mill, inda suka harbe shi da matarsa Hajiya Adama duk a Kauyen Kebberi a karamar Hukumar Malam Madori", Shiisu ya tabbatar.
Ya tabbatar da cewa sun samu wayar hannu guda biyu a inda aka yi kisan, sannan ana binciken mutum biyar da ake zargi.
Shiisu ya tabbatar da cewa suna kokari cafko wadanda suka tsere bayan aikata barnar.
No comments