Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta yi lale marhabin da matakin gwamnatin Amurka na cire kasar daga sahun wadanda take yi wa kallon masu tauye ...
Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta yi
lale marhabin da matakin gwamnatin Amurka na cire kasar daga sahun wadanda take
yi wa kallon masu tauye ‘yancin yin addini.
A cikin wata sanarwa da ya fitar,
Ministan YaÉ—a labarai da al’adu na Nijeriya, Alhaji Lai Mohammed ya kira
matakin na Amurka da adalci.
Rahotanni sun nuna cewa a jiya ne
Amurkar ta cire sunan kasar daga jerin ƙasashen da take zargi da tauye yancin
addini kwana É—aya kafin Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken ya isa Nijeriyar
a yau Alhamis.
No comments