Ministocin lafiya na kasashe bakwai masu karfin tattalin arziki a duniya da ake kira G7 za su yi wani taro domin samar da matsay...
Ministocin lafiya na kasashe bakwai masu karfin tattalin arziki a duniya da ake kira G7 za su yi wani taro domin samar da matsaya kan sabon nau'in cutar korona na Omicron.
An fara gano wannan nau'in cutar ne a Afirka ta Kudu a ranar Laraba da ta gabata kuma ana ci gaba da samun masu kamuwa da cutar.
Kasashen France da Switzerland da Canada duk sun tabbatar da bullar cutar a kasashen nasu a ci gaba da gudanar da binciken kimiyya kan wannan nau'i na annoba na Omicron.
Gwamnatin Najeriya ta ce nau’in cutar bai ɓulla a ƙasar ba kawo yanzu, kamar yadda hukumar da ke ɗakile cutuka masu yaɗuwa ta ce ta ɗauki matakai na ɗakile cutar a ƙasar kamar yadda BBC ta labarto.
No comments