Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Sunayen ‘Yan Takarar Neman Shugabancin Kasar Libiya Da Isra’ila Ke Mara Wa Baya

  Isra’ila ta nuna sha’awarta na nuna goyon bayanta ga wasu ‘yan takara guda biyu da suke neman shugabancin kasar Libya a zaben da za’a yi a...

 


Isra’ila ta nuna sha’awarta na nuna goyon bayanta ga wasu ‘yan takara guda biyu da suke neman shugabancin kasar Libya a zaben da za’a yi a watan gobe , da nufin share hanyar kulla hulda tsakaninta da gwamnati mai zuwa,

Jaridar Al-akhbar Daily ta kasar Lebanon ta fitar da wani rahoto da ke nuna cewa gwamnatin Yahudawan sahayoniya ta nuna gamsuwa da wasu ‘yan takarar shugabancin kasar ta Libya da suka hada da Janaral Khalifa Haftar da kuma Saifil Islam Ghaddafi dan tsohon shugaban gwamnatin kasar da aka kashe, a matsayin wadanda za su iya cika mata burinta na kokarin sake kulla huldar Diflomasiya da kasar.

Rahoton ya jaddada cewa ‘yan takarar shugabancin kasar guda biyu a shirye suke su daidaita alakarsu da Isra’ila kuma zai kasance wani bangare ne daga cikin shirye-shiryen da suke yi da ba a bayyana ba, domin gudun ka da lamarin ya shafi kuri’un da za su samu a lokacin zabe, musamman idan aka yi la’akari da yadda al’ummar Libya suke adawa da kulla hulda da Isra’ila kamar yadda rahoton Al-akhbar ya ce.

Wannan yana zuwa ne bayan ziyarar da babban dan Janar Khalifa Haftar ya kai Isra’ila a watan jiya, inda ya gana da jami’an gwamnatin Isra’ila kuma ya nuna gamsuwarsa da batun kulla hulda tsakanin Tel aviv da kuma Tripoli , ita kuma ta yi alwashin bawa Libya duk wani taimakon soji da na siyasa idan har aka daidaita alaka tsakani .

No comments