Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

‘‘Yan Bindiga Na Amfani Da ‘Oba-oba’ A Jihar Katsina’

Gwamnatin jihar Katsina ta ce ‘yan bindiga da ke aiki a jihar na amfani da Rediyon oba-oba wajen shawo kan matsalar rufe harkokin sadarwa ...


Gwamnatin jihar Katsina ta ce ‘yan bindiga da ke aiki a jihar na amfani da Rediyon oba-oba wajen shawo kan matsalar rufe harkokin sadarwa a jihar.

Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa, a watan Satumba ne gwamnatin jihar ta rufe hanyoyin sadarwa a kananan hukumomi 13 da ta ce suna kan gaba wajen harin ‘yan bindiga a jihar.

Sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Mustapha Inuwa, a wani taron manema labarai a ranar Alhamis, ya ce ‘yan bindigar sun jajirce wajen kaucewa matakan tsaro da aka tsara domin dakile ayyukansu.

“Duk da nasarorin da aka samu, amma ya kamata a lura da cewa tun lokacin da aka fara dokar hana mallakar kaya, ‘yan bindigar da ke fadin kananan hukumomin sun jajirce wajen samar da sabbin dabaru da nufin kaucewa tasirin umarnin, cewar Inuwa.

“Dabarun sun hada da kai hari ga masu ababen hawa da masu tuka babura zuwa kwasar man fetur daga tankunan mai, zuwa farfagandar al’umma da tursasa kauyuka zuwa samar da man fetur a madadinsu. Wani mataki na baya-bayan nan kuma mafi tayar da hankali da masu laifin suka yi shi ne yadda ‘yan fashin suka samu na Rediyon 'Frequency Walkie Talkie Transceivers'.

Sakataren gwamnatin, wanda kuma shi ne shugaban kwamitin tsaro a jihar, ya ce jami’an tsaro na kan bin sawun ‘yan bindigar da ke amfani da wayar tafi da gidanka.

Inuwa ya ce a tsakanin watan Maris zuwa Satumba, an kama mutane 480 da ake zargin ’yan bindiga ne, 42 daga cikinsu suna kan bincike, yayin da 216 ke fuskantar tuhuma.

Haka kuma bayyana cewa an samu raguwar hare-haren ‘yan ta’adda tun bayan da aka ba da umarnin tsare mutane, Mista Inuwa ya kara da cewa daga watan Satumba zuwa yau an kama mutane 244 da ake tuhuma tare da 33 da ake gudanar da bincike a kansu, yayin da 80 ke fuskantar tuhuma.

Ya ce an dauki matakan tsaro da ke cikin umarni domin magance matsalar rashin tsaro bisa dabara, yana mai cewa hakan abu ne na bukata.

“ kuma ba a sanya shi don cutar da jama’ar jihar ba ko kuma wahala. Manufar ita ce kamo yanayin da ke tasowa wanda ke zama barazana ga zaman lafiya, da rayuwar mu baki daya.”

No comments