Gwamnatin jihar Katsina ta ce ‘yan bindiga da ke aiki a jihar na amfani da Rediyon oba-oba wajen shawo kan matsalar rufe harkokin sadarwa ...
Gwamnatin
jihar Katsina ta ce ‘yan bindiga da ke aiki a jihar na amfani da Rediyon
oba-oba wajen shawo kan matsalar rufe harkokin sadarwa a jihar.
Jaridar
Dimokuradiyya ta rawaito cewa, a watan Satumba ne gwamnatin jihar ta rufe
hanyoyin sadarwa a kananan hukumomi 13 da ta ce suna kan gaba wajen harin ‘yan
bindiga a jihar.
Sakataren
gwamnatin jihar, Alhaji Mustapha Inuwa, a wani taron manema labarai a ranar
Alhamis, ya ce ‘yan bindigar sun jajirce wajen kaucewa matakan tsaro da aka
tsara domin dakile ayyukansu.
“Duk
da nasarorin da aka samu, amma ya kamata a lura da cewa tun lokacin da aka fara
dokar hana mallakar kaya, ‘yan bindigar da ke fadin kananan hukumomin sun
jajirce wajen samar da sabbin dabaru da nufin kaucewa tasirin umarnin, cewar
Inuwa.
“Dabarun
sun hada da kai hari ga masu ababen hawa da masu tuka babura zuwa kwasar man fetur daga tankunan mai, zuwa farfagandar al’umma da tursasa kauyuka zuwa samar da
man fetur a madadinsu. Wani mataki na baya-bayan nan kuma mafi tayar da hankali da
masu laifin suka yi shi ne yadda ‘yan fashin suka samu na Rediyon 'Frequency
Walkie Talkie Transceivers'.
Sakataren
gwamnatin, wanda kuma shi ne shugaban kwamitin tsaro a jihar, ya ce jami’an
tsaro na kan bin sawun ‘yan bindigar da ke amfani da wayar tafi da gidanka.
Inuwa
ya ce a tsakanin watan Maris zuwa Satumba, an kama mutane 480 da ake zargin
’yan bindiga ne, 42 daga cikinsu suna kan bincike, yayin da 216 ke fuskantar
tuhuma.
Haka
kuma bayyana cewa an samu raguwar hare-haren ‘yan ta’adda tun bayan da aka ba
da umarnin tsare mutane, Mista Inuwa ya kara da cewa daga watan Satumba zuwa
yau an kama mutane 244 da ake tuhuma tare da 33 da ake gudanar da bincike a
kansu, yayin da 80 ke fuskantar tuhuma.
Ya
ce an dauki matakan tsaro da ke cikin umarni domin magance matsalar rashin
tsaro bisa dabara, yana mai cewa hakan abu ne na bukata.
“
kuma ba a sanya shi don cutar da jama’ar jihar ba ko kuma wahala. Manufar ita
ce kamo yanayin da ke tasowa wanda ke zama barazana ga zaman lafiya, da rayuwar
mu baki daya.”
No comments