Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

YANZU-YANZU: Gwamnatin Kaduna Ta Bada Umurnin Maido Da Sadarwa A Wasu Sassan Jihar

  Daga Ammar M. Rajab   Gwamnatin jihar Kaduna ta bada umurnin a maido da sadarwa a a wuraren da aka datse sadarwar a sassan Kaduna. S...

 


Daga Ammar M. Rajab

 

Gwamnatin jihar Kaduna ta bada umurnin a maido da sadarwa a a wuraren da aka datse sadarwar a sassan Kaduna.

Samuel Aruwan, Kwamishinan lura da tsaron cikin gida shi ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a babbar Sakatariyar kungiyar ‘yan jarida ta kasa reshen Kaduna a yau Juma’a 26 ga watan Nuwamban 2021.

Samuel Aruwan ya ce gwamnatin jihar ta bai wa dukkanin hukumomin da yakamata umurnin dawo da sadarwar a inda aka datse a wadansu kananan hukumomin jihar.

A watan Oktoban 2021 ne, gwamnatin jihar ta datse sadarwar bisa shawarwarin hukumomin tsaro kan matakan da suka dauka na dakile ayyukan ‘yan bindiga da ‘yan fashin daji da sauran ayyukan bata gari a jihar. Inda Samuel Aruwan ya ce a yanzu hukumomin tsaron sun bayyanawa gwamnatin jihar cewa suna iya maido da sadarwar.

Sai dai Samuel Aruwan ya ce datse sadarwar da suka yi ya taimakawa hukumomin tsaro wajen samun wadansu nasarorin, wanda hukumomin tsaron za su bayyana a kwanan nan.

Samuel Aruwan ya ce tsawaita datsewar sadarwar zai shafi ayyuka da kasuwanci da dama na ‘yan jihar masu bin doka da oda.

Inda ya bada tabbacin cewa za a dawo da sadarwar daga yanzu zuwa ‘yan kwanaki masu zuwa. A yayin da masu sadarwar ke kokarin dawo da sadarwar kamar yadda aka umurce su.

Gwamnatin ta jinjinawa ‘yan jihar musamman wadanda datsewar sadarwar ya shafa bisa hakuri da sadaukarwar da suka nuna.

Sai dai ya ce har yanzu dokar hana sayar da man fetur a jarka, da na hana hawa babur, da haramta cin kasuwanni na mako-mako da safarar shanu na nan a wadannan kananan hukumomi da aka ayyana. 

No comments