Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

YANZU-YANZU: Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Matsaya Da ASUU

  Daga Muhammad Farouk Gwamnatin Tarayya da kungiyar Malaman Jami’o’i sun cimma matsaya bayan da Kakakin majalisar Tarayya, Femi Gbajabiamil...

 


Daga Muhammad Farouk

Gwamnatin Tarayya da kungiyar Malaman Jami’o’i sun cimma matsaya bayan da Kakakin majalisar Tarayya, Femi Gbajabiamila ya shiga tsakani kamar yadda majiyarmu ta Daily Trust ta labarto.

An cimma matsayar ne a wani zaman sulhu da aka yi a majalisar kasa a Abuja a yau Alhamis.

Kakakin majalisar ya gayyaci ministan ilimi, Mallam Adamu Adamu, minister kudi, Zainab Ahmed, da kuma jagororin ASUU din domin zaman sulhu don dakile tafiya yajin aikin.

A yayin zaman, an yi bitar yarjejeniyar da gwamnatin Tarayya ta cimma da ASUU din tun 2009.

A jawabinsa, Kakakin majalisar, Femi Gbajabiamila, ya ce majalisar ba za ta zura ido abubuwa na tabarbarewa ba tsakanin ASUU da gwamnatin Tarayya. Ya ce; ‘yan Nijeriya ba za su sake iya jurewa wani sabon yajin aikin ba, sannan kuma bai kamata ASUU su ci gaba da amfani da yajin aiki a duk lokacin da suke so a biya bukatunsu ba.

Ya ce; dole ne bangarorin biyu a jingina musu laifin kasa shawo matsalar da ya ki ci ya ki cinyewa. Sai dai ya ce tabbas ASUU ta yi hakuri da gwamnati sosai, a don haka akwai bukatar gwamnati ta girmama yarjejeniyar da suka yi.

A na shi martanin, shugaban ASUU, Farfesa Victor Emmanuel, ya ce akwai batutuwa da yawa da yarjejeniya da gwamnati ta yi alkawari, amma a cewarsa abin takaici ne na yadda gwamnatin ta ki cika alkawuran da ta yi da ya hada da alawus, kayayyakin more rayuwa, amfani da UTASS a maimakon IPPIS da sauran su wanda ya ce sune abin da ke sanya kungiyar tafiya yajin aiki.

Ya ce sun cimma yarjejeniya da gwamnati ta Naira Tiriliyan 1.3 za a bai wa kungiyarsu wanda za a yi amfani da kudaden wajen bunkasa kayayyakin karatu da sauran abubuwan dake da bukatar kudi. A cewarsa, sun amince za a biya kudaden daki-daki, inda za a far aba su naira biliyan 200 wanda ya ce ba a biya ba har yanzu.

Ya ce kudin ma daga bayan an dawo da shi naira biliyan 52.127 inda Naira biliyan 30 na  kayayyakin more rayuwa da kuma naira biliyan 22.127 na alawus na Malamai, wanda ya ce ba ko daya da gwamnati ta biya.

A na shi jawabin, ministan ilimi, Henry Nwajuba, ya ce dukkanin abubuwan da ASUU ta fada gaskiya ne, kuma gwamnati ta fara daukar matakin biyan bukatun nan musamman batun alawus da kuma kudaden more rayuwa.

Ita ma ministar kudi, Zainab Ahmed ta ce akwai batun biyan, kuma ma a yanzu haka akwai wadansu kudaden a kasa wanda a cewarta za su biya a cikin mako.

Bayan ministocin biyu sun kammala bayani, jagororin ASUU sun amince da sabon alkawarin, inda suka ce za su bibiya har zuwa wa’adin da suka diba ta tafiya yajin aiki.

 

No comments