Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Asibitoci Na Cika Makil Saboda Masu Dauke Da Cutar Korona A Jamus

Mahukuntan Jamus za su takaita wasu harkoki na walwalar wadanda ba su yi allurar rigakafi ba, a yankunan da asibitoci ke cika da...


Mahukuntan Jamus za su takaita wasu harkoki na walwalar wadanda ba su yi allurar rigakafi ba, a yankunan da asibitoci ke cika da masu corona.

DW ta labarto cewa; shugabanni na tarayya da jihohin kasar 16, a wani taron da suka gudanar a ranar Alhamis suka cimma wannan matsaya na ba-sani-ba- sabo, wanda ke zama martani ga barazanar sake ta'azzarar cutar corona a karo na hudu a Jamus.

Daga yanzu sai wanda ke da shaidar yin allura ko kuma bai jima da warkewa daga cutar ba ne, zai iya shiga wuraren wasanni ko cin abinci da makamantansu a yankuna da cutar ta fi kamari.

Saxony, ita ce jihar da ta fi kowacce shiga cikin wadi-na-tsaka-mai wuya na yaduwar cutar coronar a karo na hudu, tuni kuma ta fara la'akari da kafa dokar kulle tare da rufe mafi yawan wuraren shakatawa.

Jihar ce dai aka fi samun karancin masu allurar rigakafi a yankin gabashin Jamus, kuma ke da mafi yawan wadanda suka kamu da COVID 19 a cewar rahoton. 

No comments