Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Ba Zan Yi Watsi Da Alƙawuran Da Na Yi Wa Ƴan Nijeriya Ba – Buhari

  Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayyana cewa gwamnatinsa ba za ta yi watsi da duk alkawuran da ta yi ba lokacin yakin neman zaɓe kafin ...

 


Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayyana cewa gwamnatinsa ba za ta yi watsi da duk alkawuran da ta yi ba lokacin yakin neman zaɓe kafin cikar wa’adinsa.

Shugaban ya bayyana haka ne a sakonsa na Kirsimeti ga ’yan Nijeriya, inda ya ce yana taya Kiristoci a Najeriya farin ciki kamar sauran mabiya a duniya don gudanar da bikin a wannan shekarar.

A cikin saƙon, shugaban ya roƙi ƴan Nijeriya su yi rigakafin korona domin rage bazuwar annobar.

Ya kuma taɓo batun tsaro inda ya ce duk da nasarorin da jami’an tsaro suka samu amma har yanzu akwai ƙalubale.

“Ina kira ga ƴan Najeriya da su yi imani da mu da kuma ɗaukar abubuwan da ke faruwa a matsayin wani lokaci da kuma zai wuce, kamar sauran yanayi marar daɗi a tarihin ƙasar.”

“Wannan gwamnatin ba za ta yi watsi da alƙawullan da ta yi wa ƴan Nijeriya ba,” in ji shugaban.

 Tushe: BBC

No comments