Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Iran Ta Dage Kan Dole Ne A Cire Mata Takunkumin Da Aka Kakaba Mata

  Iran dage akan dole ne fa a cire mata takunkumin da aka kakabata mata. Iran din ta ce ya kamata tattaunawar nukiliyar da aka koma a jiya r...

 


Iran dage akan dole ne fa a cire mata takunkumin da aka kakabata mata. Iran din ta ce ya kamata tattaunawar nukiliyar da aka koma a jiya ranar Litinin tsakaninta da wakilan manyan kasashen duniya a birnin Vienna, ta mayar da hankali ne kan batun dage wa kasar takunkumin da aka kakaba mata da kuma tabbatar da cewa Amurka za ta dawo a cikin yarjejeniyar da aka cimma a baya.

Duk da wannan fata na Iran, Kungiyar Tarayyar Turai ta ce tattaunawar abu ne mai cike da sarkakiya.

Tattaunawar ceto yarjejeniyar nukiliyar Iran da aka kulla a shekarar 2015, ta sake komawa a karshen watan Nuwamba, bayan da aka shafe watanni 5 ana tattaunawa bayan zaben shugaban kasar Iran Ebrahim Raisi.

Zaman tattaunawar na neman dawo da Amurka ne, bayan ta fice daga yarjejeniyar a shekarar 2018 karkashin shugaba Donald Trump na wancan lokacin tare da kara kakabawa kasar takunkumi.

Gabanin ci gaba da shirin tattaunawar, Ministan Harkokin Wajen Iran Hossein Amir-Abdollahian, ya ce ya kamata a sabunta yarjejeniyoyin da kuma tabbatar da dage takunkumin da Amurka ta kakaba wa kasarsa idan fadar White House ta koma kan wannan yarjejeniya.

Bude zagaye na takwas na tattaunawar ya kunshi tawagogi daga Iran da sauran kasashen da suka rage a yarjejeniyar da suka hada da Birtaniya, Chana, Faransa, Jamus, da kuma Rasha.

Fadar White House dai na taka rawa a kaikaice tare da jami'an Diflomasiyya da ke ci gaba da kai-komo tsakanin bangarorin Iran da Amurka.

Yarjejeniyar nukiliyar da aka cimma a shekara ta 2015 ta bayar da damar dage takunkumin tattalin arziki da aka kakaba wa Iran.

No comments