Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Kasarnan Na Da Kyakkyawar Makoma Idan Al’umma Ta Tashi Tsaye, Inji Shaikh Zakzaky

Daga Ammar M. Rajab Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya bayyana cewa; kasarnan tana da kyakkyawan makoma a gaba amm...



Daga Ammar M. Rajab

Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya bayyana cewa; kasarnan tana da kyakkyawan makoma a gaba amma sai al’umma ta tashi tsaye ta nemi wannan kyakkyawar makomar daga hannun masu rike da madafun iko da ya bayyana cewa sam ba su damu da abin da ya dami al’umma ba. Shehin Malamin ya bayyana hakan ne a ranar Lahadin 12 ga watan Disambar 2021 a taron tunawa da waki’ar Zariya da ta auku shekaru shida da ya gabata. Taron ya gudana ne a Yesmin Event Centre dake Gwagwalada a Birnin Tarayya Abuja. Shehin Malamin ya gabatar da jawabinsa ne daga gidansa dake Abuja, inda aka haska jawabin ta hanyar majigi.  

Tun a farkon jawabinsa, Shaikh Zakzaky ya fara ne da cewa; “Na so a ce ina tare da ku don na koya daga sauran mutane kafin na bayar da nawa gudunmawar, amma duk daya; Ina taya ku murna da kuka taru a yau kan wani al'amari mai matukar muhimmanci a rayuwar dan Adam - wato batun hakkin dan Adam. Shakka babu, dan Adam an tsara su rayu a tare, kuma zaman taren ya zame musu wajibi ('yan Adam) ya zama suna da dokoki, ka'idoji da zai gudanar da rayuwarsu.”

Shehin Malamin ya ci gaba da cewa; “Kuma mafi muhimmancin cikin dukkannin hakkokin shi ne ‘yancin gudanar da rayuwa (hakkin kowane mutum ne da ya sami kansa a raye). Babu wanda zai iya daukar ransa sai dai a tsarin shari'a - ma'ana idan ya dauki ran wani to lamari ne da ya zama dole shima a dauki ransa, idan ba don wannan ba, ba za a dauki ran kowa ba”, ya nusasshe.

Har wala yau Shaikh Zakzaky ya ci gaba da cewa; “Wannan ‘yancin gudanar da rayuwar wanda ya hada da wasu hakkoki, duk yana cikin kundin tsarin mulkin Nijeriya, wanda masu rike da madafun iko a kodayaushe suke rantsuwar kare su. Suna yin rantsuwa da littattafai masu tsarki wadanda suka yi imani da su (Alkur'ani, da baibul). Kaico, mun samu kanmu a cikin al’umma a yau, ‘yancin wannan rai din ana daukarsa; wadanda suke rike da madafun iko suna ganin suna da ‘yancin kashe wani a kowanne lokacin da suka ga dama, kisan gilla ya zama ruwan dare. Hukumomin tsaro da aka dauke su domin su kare doka yanzu ana amfani da su (daga wadanda suke rike da madafun iko) domin karya wannan doka din”, ya lurantar.

“Jami’ai cikin khakinsu ana aika su su aikata ta'addanci a kan mutane. Sojoji da ’yan sanda da ma ’yan sandan sirri da ba sa sanye da khakinsu, a gaskiya ma a zamanin nan suna sanya rigar ta’addanci (ma’ana suna boye fuskokinsu kamar yadda ‘yan ta’adda ke yi). Gwamnati ta zama makamin aikata ta’addanci, ta koya wa jama’a su zama ‘yan tashin hankali! An tilasta wa mutane, saboda yanayi, su ma su zama ‘yan tashin hankali (saboda ita ma gwamnati ta zama ‘yar tashin hankali).

“Sakamakon haka, muna bayani ne kan hakkin dan adam, yakamata mu fahimci cewa wannan al'umma ba za ta taba kasancewa cikin tsari ba har sai wadanda suke rike da madafun iko suna mutunta hakkin sauran mutane ba. Masu mulki suna ganin su ne shari'a- suna ganin su sun fi karfin doka; a don haka za su iya daukar ran kowa a kowanne lokaci. Ba su damu da yawan magana, wa'azi ko nasiha ba (wanda ake yi  saboda su); ba su damu ba, ba ruwansu da abin da ke faruwa da sauran mutane”, ya jaddada.

Ya kara da cewa; “Dubi abin da ke faruwa a cikin wannan al'umma a yau, wanda aka ce kowa yana cikin yanayin tsoro, ciki har da wadanda suke cikin masu rike da madafun iko – domin su ma ba za su taba samun zaman lafiya ba idan sauran mutane ba su samu zaman lafiya ba! A don haka, babban hakkin da kowa ya kamata ya kiyaye shi, shi ne ‘yancin gudanar da rayuwa, ba ku da ‘yancin kashe rayukan wasu; Ba ku ma da ikon kashe na ku rayukan- babu wanda ke da ikon kashe kansa. Baku da ‘yancin zubar da ciki saboda da a ce mahaifiyarka ta zubar da cikinka, da ba ka rayu ba. Babu wanda ke da hakkin ya dauki ran kowa!

“Haka nan, tun da muna magana ne game da ‘yancin ‘yan adam, akwai hakkin muhalli, hakkin dukkan halittu - ciki har da dabbobi (suna da hakki). Matattu ma suna da hakki- ‘yancin a girmama su bayan mutuwarsu tare da yi musu jana'izar da ta dace da imaninsu, dokoki da al'adunsu”, ya tabbatar.

Har wala yau Shaikh Zakzaky ya kara da cewa; “Amma a zamanin yau, sai ka ga masu rike da madafun iko suna tunanin za su iya kashewa tare da kona gawarwakin (mutane), ko kuma su dauke su zuwa inda ba a san inda suke ba, tare da bizne su a kabarin  bai daya. Kisan kiyashin da ya faru a Zariya shekaru shida da suka gabata misali ne a nan, inda a cikin kwanaki uku sojojin Nijeriya suka killace birnin Zaria (ciki har da duk hanyoyin shiga cikin birnin), inda suka kashe sama da mutum dubu daya tare da kwashe gawarwakinsu. kuma a bizne su a kaburbura daban-daban. A kan wannan, sun kuma kama mutane kusan dari biyar bisa “zargin kisan kai” na soja daya. Tabbas, dukkannin kotunan sun sallamesu tare da wanke dukkan wadanda aka gurfanar da su a gabansu”, ya lurantar.

Ya jaddada cewa; “Ku dubi yadda masu rike da madafun iko suka so goge hatta hujjojin wannan danyen aiki da suka aikata. Wannan shi ne mataki na farko da wannan gwamnati (hukuma) ta dauka, kuma daga baya za ku iya ganin yadda kisan gilla ya zama ruwan dare a yau. Yanzu mutane suna rayuwa cikin tsoro da firgici a ko’ina. Ba za ka kashe wasu ba, ka kuma yi tsammanin ka zauna lafiya, sun riga sun aikata (ta hanyar kisan kiyashin Zariya) sun murkushe zaman lafiya!

“Muna da bukatar mu sake tunani game da gabanmu; wasu suna tambayata ko akwai wata kyakkyawar makoma ga kasar nan? Nace akwai! Ba muna rayuwa ne a cikin al’umma marar fata ba, tabbas akwai fata (ga Nijeriya), amma fatan ya ta’allaka ne a kan mutane ba akan masu rike da madafun iko ba. Ba mu da fata daga wurin masu rike da madafun iko, domin ba ruwansu da abin da ke faruwa ga al’umma. Amma yakamata al’umma ta tashi ta nemi kyakkyawar makoma ga al'ummarmu. Muna fatan nan gaba kadan abubuwa za su iya sauyawa zuwa kyakkyawa- wannan shi ne fatanmu. Kuma Allah Ya taimake mu baki daya. Nagode sosai”, ya karkare.

Kamar dai yadda aka saba a duk shekara ana gudanar da irin wannan taron na tunawa da kisan kiyashin sojojin Nijeriya wanda suka aikata akan ‘yan’uwa Musulmi almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky a ranekun 12 zuwa 14 ga watan Disambar 2015, inda ya fara gudana a Zariya a 2016, sannan aka yi a Keffi dake jihar Nasarawa a 2017, sai kuma aka yi a Suleja ta jihar Neja a shekarar 2018, a shekarar 2019 kuma, taron ya gudana ne a garin Katsina, inda a shekarar 2020, aka gudanar da taron a garin Ayingba ta jihar Kogi. A bana ma ba a yi kasa a guiwa ba, a inda da safiyar ranar Lahadin 12 ga watan Disambar 2021 aka gudanar da gagarumin taron tunawa da kisan kiyashin sojojin.

Tunda fari bayan bude taro da addu’a, karatun Alkur’ani mai girma, an gudanar da ‘Display’ daga Kashshaful Imam Mahdi da Intizar da sauran su. An kuma gudanar da wakokin juyayin munasabar wanda Shamsu Fudiyya da Alhaji Mustapha Gadon {aya suka yi a lokuta daban-daban.

Farfesa Isa Hasan Mshelgaru, daga Jami’ar Ahmadu Bello dake Zariya, shi ne mai jawabi na farko a taron, inda ya yi jawabi kan; ‘hujjoji da adadin mata da kananan yara da sojoji suka yi wa kisan kiyashi a Zariya’.

Malama Ruhi Rizvi daga Birtaniya ita ce ta kasance mai jawabi na biyu, inda ta yi jawabi kan; ‘nazarin martanin kasashen duniya kan kisan kiyashin Zariya wanda aka haska ta hanyar majigi’.

Mai jawabi na uku a taron shi ne; mai rajin kare hakkin bil’adama, kuma shugaban kungiyar ‘Concerned Nigerians’, Prince Deji Adeyanju, ya yi jawabi a kan maudu’i mai taken’ “matakan tunkarar take hakkin dan Adam.” Shima an haska ne ta hanyar majigi. Bayan Deji Adeyanju ya kammala jawabinsa, Farfesa Abdullahi [anladi daga Jami’ar Ahmadu Bello Zariya ne ya yi ta’aliki kan jawabinsa.

Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ne ya gabatar da jawabin rufe taron, wanda aka haska ta hanyar majigi ga mahalarta taron. A yayin gabatar da Shaikh Zakzaky (H), wanda Injiniya Abdullahi ya yi, wakilinmu da ya halarci taron ya lura da yadda wurin taron ya kaure da kabarbari da salatin Annabi saboda shauki da sauraren jagoran Gwagwarmayar Musulunci.

Dukkanin jawaban an gudanar da su ne a harshen Turanci. Kuma taron ya samu halartar dimbin ‘yan’uwa maza da mata, yara da kanana daga sassa daban-daban na kasarnan.

Daga karshe, Shaikh Sunusi Abdulkadir ne ya rufe taron da addu’a.

A ranar Litinin 13 ga watan Disambar kuwa, taron ya gudana ne a muhallin Fudiyyah Maraba dake karamar Hukumar Karu ta jihar Nasarawa mai makwabtaka da Birnin Tarayya Abuja. Inda aka saurari waken juyayin wannan waki'a tare da sauraren bayanai daga wasu daga cikin ganau na waki'ar.

A ranar Talata, 14 ga watan Disamba, ranar ce a kawo karshen tarukan na kwanaki 3 da aka gabatar, inda taron ya gudana a garin Suleja ta jihar Neja dake makwabtaka da Birnin Tarayya Abuja.

Idan ba ku manta ba, Dandalin Academic Forum, Sisters Forum da kuma Mu’assatus Abdul Fadl Abbas ne suke shirya taron a madadin Harkar Musulunci a Nijeriya a duk shekara.

 

No comments