Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Ku Iya Bakinku -Sakon DSS Ga Malamai, Sarakuna Da 'Yan Siyasa

Hukumar tsaro ta farin kaya ta Najeriya DSS, ta gargaɗi ƴan ƙasar ciki har da sarakunan gargajiya da ƴan siyasa da malaman addin...


Hukumar tsaro ta farin kaya ta Najeriya DSS, ta gargaɗi ƴan ƙasar ciki har da sarakunan gargajiya da ƴan siyasa da malaman addinai da cewa su guji yin duk wani abu da zai jawo saɓa doka da oda.

A wata sanarwa da ta fitar ranar Talata mai ɗauke da sa hannun mai magana da yawunta PN Afunanya, DSS ta ce ta yi wannan gargaɗi ne don fahimtar da ta yi na yadda wasu mutane ke neman mulki ido a rufe da suke amfani da hanyoyin da ba su dace ba ta wajen tunzura ƴan ƙasa da kuma ruruta wutar siyasa.

Wannan sanarwa ta DSS ta zo ne a daidai lokacin da yanayin rashin tsaro ke ƙara ta'azzara musamman a arewacin Najeriya, inda mutane da dama ke nuna fushinsu kan abin da suke kira gazawar gwamnati wajen kasa magance matsalar.

Sanarwar ta ce: "Tuni masu irin wannan aƙida sun fara siyasantar da batun rashin tsaro a wasu sassan ƙasar bisa wasu dalilai na son kansu.

Da yawansu suna amfani da damar yanayin da ake ciki don jawo rarrabuwar kawuna a tsakanin ƴan ƙasa, da neman suna da ko kuma sanya ƙasar cikin matsala."

Ga dai saƙonnin da ke ƙunshe a cikin sanarwar kamar haka:

Hukumar ta gargaÉ—i dukkan masu hannu cikin irin waÉ—ancan laifuka da ta ambata da su guji aikata su.

Ta kuma nemi ƴan siyasa da su yi komai bisa doka tare da gujewa maganganu ko ayyukan da za su iya kunna wutar rikici gabanin zaɓukan shekarar 2023.

"Masu saita tunanin al'umma kamar malamai da sarakunan gargajiya ma ana buƙatar su iya bakinsu su kuma guji kalaman tunzura mutane," in ji saƙon.


Lokutan bukukuwan ƙarshen shekara

Saƙon DSS ya ce kamar yadda aka sani ne bara-gurbi kan zafafa ayyukansu kafin lokuta da kuma bayan bukukuwan ƙarshen shekara.

Don haka ne ta yi kira ga shugabannin al'umma da masu otel-otel da masu kula da kasuwanni da tasoshi da wuraren shaƙatawa da su dinga taka tsantsan tare da kasancewa a ankare da duk wani motsi da ba su gamsu da shi a wurarensu, kamar wuraren ibada da kasuwanni da masarautu da makarantu da sauran wuraren taruwar jama'a.

Hukumar ta yi kira ga masu kula da wadannan wurare da su yi ƙoƙarin kai rahoto ga hukumomin tsaro kan duk abin da ba su gamsu da shi ba.

Ta ce shafin intanet ɗinta da layukan wayarta na kai ƙorafi za su kasance a buɗe ga al'umma.

Short presentational grey line

Kula da yara a lokacin hutu

A yayin da makarantu suka yi hutu ɗalibai suka koma gida don yin hutu, akwai yiwuwar ɓata-gari za su yi ƙoƙarin sanya su cikin munanan ayyukansu in ji hukumar DSS.

Ta lissafa 'munanan abubuwa' kamar su sata da fashi da rashin ɗa'a da zanga-zanga da shaye-shayen munanan ƙwayoyi da satar mutane kan kuɗin fansa.

A don haka ne hukumar ta yi kira ga iyaye da su sa ido kan ayyukan da Æ´aÆ´ansu ke aikatawa don hana su yin abubuwan da ba su dace ba.

"Baya ga É—alibai, Æ´an majalisar jihohi da na tarayya da ma'aikatan gwamnati da na kamfanoni ma da ke hutu na iya fuskantar barazana da dama.

"Wannan ya kuma shafi ƴan Najeriya da mai yiwuwa su yi tafiye-tafiye a ciki da wajen ƙasar don yin bukukuwan tare da su."

Short presentational grey line

GargaÉ—i ga masu satar mutane

WaÉ—ancan mutanen na sama da hukumar ta yi magana a kansu na iya fuskantar barazanar sace su da kashe su ko kuma amfani da su a siyasance ta hanyar da ba ta dace ba, in ji DSS.

"Don haka muna kira a gare su da su zama masu taka tsantsan ta yadda ba za su faÉ—a hannun waÉ—ancan bara-gurbin ba."

DSS ta jaddada gargaÉ—inta ga Æ´an bindiga da masu satar mutane da Æ´an ta'adda da dukkan wasu masu kai hari kan hukumomin tsaro da fararen hula da cewa gara su sake tunanin.

"Waɗannan mutanen walau a arewa suke ko a kudu sun san kansu. Babu shakka sun tsallake iyakoki kuma yanzu lokaci ya yi da za a murƙushe su."

Short presentational grey line

Batun Nnamdi Kanu

Hukumar DSS ta kuma taɓo batun jagoran ƴan awaren Biafra wato Nnamdi Kanu, inda ta musanta batutuwan da ake cewa tana gallaza masa a yayin da yake tsare.

"A baya ba ma magana ne kan Kanu ba don tsoron kowa ko komai ba sai don gudun jawo ce-ce-ku-ce. Amma a yanzu albarkacin ƙeƙe da ƙeƙe da girmama dimokraɗiyya ne hukumar taken son fayyace abubuwa."

  • DSS ta yi watsi da zargin cewa tana muzgunawa Kanu
  • An samar masa da dukkan kayan alatun da yake buÆ™ata irin wanda ba za a same su a ko ina ba a faÉ—in Æ™asar
  • An ba shi cikakkiyar damarsa Æ´ancinsa
  • Ba a taÉ“a hana shi damar ibada ba
  • Ana ba shi damar ganin Æ™wararrun likitoci masu duba lafiyarsa. "Shi da kansa Kanu ya tabbatarwa da masu ziyartarsa cewa ba a taÉ“a muzguna masa ba."
  • Maganar cewa ana barinsa da yunwa ma Æ™age ne. Abinci sai wanda ya zaÉ“a ake ba shi.
  • Batun ba a barinsa ya sauya kaya Æ™arya ne. 

Kafafen yaÉ—a labarai

Sanarwar ba ta kammala ba sai da ta taɓo kafafen yaɗa labarai ta hanyar tunatar da su aikinsu a fannin tsaron ƙasa.

Ta yi kira ga Æ´an jarida a matsayinsu na masu faÉ—a a ji da su yi amfani da kafafensu wajen samar da zaman lafiya.

"Dole su mayar da hankali wajen haɗin kan ƙasa da gujewa labaran ƙarya da na tunzuri da kalaman ƙiyayya.

"Dole ƴan jarida su zama masu kishin ƙasa da yin komai bisa gaskiya a rahotanninsu."

Short presentational grey line

Sauran ƴan ƙasa

Su ma sauran ƴan ƙasa hukumar DSS ta nemi da su haɗa kai da hukumon tsaro don tabbatar da zaman lafiya a ƙasar.

Su kuma guji yaɗa duk wani abu da zai jawo karyewar doka da oda. Sannan su lira da ayyukan da zau aiwatar a lokutan bukukuwan ƙarshen shekara.

Baya ga dukkan gargaɗin da hukumar tsaro ta farin kayan ta bayyana, a ƙarshe ta ce ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen ɗaukar mataki kan duk wanda ya so kawo cikas ga zaman lafiya da tsaron ƙasa kamar yadda doka ta tanada.


-Rahoton BBC Hausa

No comments