Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Kwalara Ta Fi Kashe 'Yan Nijeriya Fiye Da Korona, Inji NCDC

Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa ta Nijeriya, NCDC ta bayyana cewa, cutar kwalara ta fi kashe jama’a fiye da annobar korona...


Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa ta Nijeriya, NCDC ta bayyana cewa, cutar kwalara ta fi kashe jama’a fiye da annobar korona musamman a wannan shekara ta 2021 a kasar.

Darakta Janar na  Cibiyar ta NCDC, Ifedayi Adetifa ya bayyana cewa, Nijeriya ta samu adadin mutanen da ya zarta  dubu 3 da 600 da suka rasa rayukansu a dalilin annnobar amai da gudawa ko kuma kwalara a cikin watanni 11 da suka gabata.

A game da annobar korona kuwa, kimanin mutane dubu 2 da 977 ne suka rasa rayukansu tun daga farkon shekarar bara zuwa wannan lokaci, kamar yadda Mista Adetifa ya yi karin bayani.

Jami’in na hukumar NCDC na bayani ne a yayin wata hira da ya yi da kafar Talabijin ta Channels, inda ya yi  bayani game da sabon nau’in cutar korona da ake kira Omicron da ya bulla a Nijeriya.

A cewarsa, yanzu haka sun dukufa ne wajen takaita yaduwar cutar kwalara duk da cewa, a halin yanzu, mutane sun fi karkata hankulansu kan annobar korona.

A bangare guda, Mista Adetifa ya  kara a cewa, tuni suka fara kintsawa domin tunkarar kakar ciwon sankarau, yana mai cewa, sun tanadi ma’aikata tare da horas da su don gudanar da aikinsu na wayar da kan al’umma.

No comments