Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Pages

Labarai:

latest

Zaben Gambia Zai Fayyace Makomar Yahya Jammeh

  Al'ummar Gambia na shirin kada kuri'a don zaben shugaban kasa a gobe Asabar, zaben da zai fayyace makomar tsohon shuga...

 


Al'ummar Gambia na shirin kada kuri'a don zaben shugaban kasa a gobe Asabar, zaben da zai fayyace makomar tsohon shugaban kasar Yahya Jammeh wanda ke zaman gudun hijira a wata kasa kamar yadda gidan Rediyon Faransa ya labarto.

Wasu masharhanta na ganin cewa manyan batutuwan da za su yi tasiri wajen zaben ‘yan takarar da za su fafata a zaben na Gambia baya ga sha’anin tattalin arziki, sun hada da makomar tsohon shugaba Jammeh wanda ya mulki kasar tsawon shekaru 22 daga shekarar 1994, dangane da yiwuwar dawowarsa daga gudun hijira, da kuma yadda zai mayar da martani ga laifukan da ake zarginsa da aikatawa a karkashin mulkinsa wadanda suka hada da fyade, azabtarwa, da kuma kisan gilla.

An tilasta wa Jammeh gudun hijira zuwa Equatorial Guinea ne a shekara ta 2017, bayan da shugaba Adama Barrow, ya kayar da shi a zaben da suka fafata sakamakon da fari tsohon shugaban ya so yin watsi da shi.

Sai dai har yanzu Jammeh na da sauran goyon bayan siyasa a Gambia, inda masu fafutukar kare shi suka matsa kaimi kan ya koma gida, yayin da kuma a gefe guda, tsohon shugaban ya nemi yin tasiri a zaben na gobe Asabar da zai gudana, inda ya yi jawabi ga gangamin magoya bayansa.

Lokaci ne dai kawai zai fayyace makomar siyasar Gambia a zaben da ke zaman zakaran gwajin dafin sabuwar dimokradiyyar kasar.

No comments