Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

'Yan Bindiga Sun Bi 'Yan Sanda Har Sansaninsu A Jihar Neja

Rfi ta labarto cewa 'yan bindiga sun kai samame wani sansanin ‘yan sandan kwantar da tarzoma a garin Ishau, na karamar hukum...


Rfi ta labarto cewa 'yan bindiga sun kai samame wani sansanin ‘yan sandan kwantar da tarzoma a garin Ishau, na karamar hukumar Paikoro ta jihar Neja, inda suka kashe jami’a 3.

Jaridar ‘Daily Trust’ da ake wallafawa a kasar ta ruwaito cewa ‘yan bindigar suna wucewa ne, inda suka yi kicibis da wata tawagar ‘yan sanda da ke sintiri, nan ne fa aka fara bai wa hammata iska a tsakaninsu.

Majiyoyi sun ce barayin dajin na barin jihar Neja ne zuwa Kaduna, sai suka yi amfani da damar wajen kaddamar da hare hare a kan al’ummomin da ke iyakokin jihohin biyu.

Kokarin samun karin bayani daga rundunar ‘yan sandan jihar Nejar ya ci tura.

No comments