Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Harin Jirgin Kasa: Shugaba Buhari Ya Yi Allah-wadai Da Harin

  Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana bakin cikinsa kan harin da ‘yan ta’adda suka kai kan jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja a ranar Liti...

 


Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana bakin cikinsa kan harin da ‘yan ta’adda suka kai kan jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja a ranar Litinin da ta gabata, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama.

Shugaban kasar a ranar Talata ya ce ya damu matuka da harin, wanda shi ne irinsa na biyu a ‘yan kwanakin nan.

Buhari ya yi Allah-wadai da harin bam da aka kai kan jirgin fasinjan, yana mai bayyana hakan a matsayin “al’amari mai matukar kaduwa.”

“Harin da aka kai kan jirgin kasan, abin takaici ne; kuma muna jajantawa iyalan wadanda suka rasu da kuma wadanda suka samu raunuka,” in ji shugaban a wata sanarwa da babban mai taimaka masa na musamman, Malam Garba Shehu ya fitar.

Buhari ya ba da umarnin a gaggauta kammala dukkan matakai na aiwatar da tsaro kan hanyoyin jiragen kasa na Abuja zuwa Kaduna da Legas zuwa Ibadan.

Ya kuma umurci hukumar kula da layin dogo ta Nijeriya da su gaggauta gyara layukan da suka lalace tare da ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum ba tare da bata lokaci ba.

“Shugaban ya bayar da wadannan umarnin ne a Abuja, Talata, bayan ganawarsa da hafsoshin tsaro karkashin jagorancin babban hafsan tsaro na kasa, Janar Lucky Irabor; da babban hafsan sojin kasa, Laftanar-Janar Faruk Yahaya; da  shugaban hafsan sojin sama, Air. Marshal Isiaka Amao; da  Sufeto Janar na ‘yan sanda, Usman Baba; da Manjo Janar Samuel Adebayo, shugaban hukumar leken asiri na tsaro; da kuma babban daraktan hukumar tsaro ta farin kaya, DSS, Yusuf Magaji Bichi a fadar gwamnati,” inji sanarwar.


No comments