Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Kwankwaso Ya Jefar Da Lema Ya Cafki Kayan Marmari

  Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso ya kawo karshen zamansa a cikin Jam’iyyar PDP mai alamar lema, inda ya sanar da ficewarsa ...

 


Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso ya kawo karshen zamansa a cikin Jam’iyyar PDP mai alamar lema, inda ya sanar da ficewarsa daga cikin jam’iyyar.

Kwankwaso ya rubuta wa shugaban mazabarsa inda ya bayyana godiya akan mu’amala mai kyau da suka yi a shekarun da ya kwashe suna aiki tare a matakin mazaba, karamar hukuma, jiha da kuma kasa baki daya.

Tsohon gwamnan ya ce sakamakon wasu dalilai na rashin fahimtar juna, ya yanke hukuncin ficewa daga jam’iyyar daga ranar Talata, 29 ga watan Maris na shekarar 2022.

Kafin dai wannan lokaci an dade ana rade radin cewar Kwankwaso zai sauya sheka zuwa Jam’iyyar NNPP mai alamar kayan marmari domin tsayawa takarar zaben shugaban kasa a shekara mai zuwa.

Tuni wasu daga cikin magoya bayansa suka fice daga PDP domin komawa sabuwar Jam’iyyar a jihar Kano da kuma wasu jihohi dake cikin kasar.


No comments