Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Nijeriya Ba Za Ta Je Qatar Gasar Kofin Cin Duniya Na 2022 Ba

  Tawagar ‘yan wasan Super Eagles ta Nijeriya ta kasa samun tikitin zuwa gasar cin kofin duniya da kasar Qatar za ta karbi bakunci a wannan ...

 


Tawagar ‘yan wasan Super Eagles ta Nijeriya ta kasa samun tikitin zuwa gasar cin kofin duniya da kasar Qatar za ta karbi bakunci a wannan shekarar.

Nijeriya ta kasa samun tikitin ne bayan tashi wasa 1-1 da tawagar kasar Ghana a wasan da suka fafata a filin wasa na Moshood Abiola dake babban birnin Tarayya Abuja.

A wasan farko dai da suka fafata a birnin Kumasi na Ghana kasashen biyu sun tashi wasa babu ci yayin da aka tashi 1-1 a wasan da suka fafata a daren jiya.

Da wannan sakamakon, kasar Ghana ta samu tikitin zuwa gasar cin kofin duniya inda za a zama daga cikin wadanda za su wakilci Afirka.

Nijeriya dai ta samu nasarar zuwa gasar cin kofin duniya da aka buga a kasar Russia a shekarar dubu biyu da sha takwas.


No comments