Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Buhari Ya Kammala Tarwatsa Rayuwar 'Yan Nijeriya, Cewar Bishop Kukah

  Rfi Hausa ta labarto cewa; Babban Limamin mabiya darikar Katolika dake Sokoto, Bishop Mathew Hassan Kukah ya bayyana cewar shugaban kasa M...

 


Rfi Hausa ta labarto cewa; Babban Limamin mabiya darikar Katolika dake Sokoto, Bishop Mathew Hassan Kukah ya bayyana cewar shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kammala lalata duk wani bangare na rayuwar jama’ar kasar a karkashin gwamnatinsa tare da bai wa cin hanci da rashawa damar habaka.

Yayin da yake gabatar da sakon bikin Easter a mujami’ar sa, Kukah ya ce duk wani bangaren rayuwar jama’ar Najeriya ya lalace, yayin da kasar ta zama sashen gobe da nisa na asibiti dauke da tarin marasa lafiya.

Limamin ya ce zukatan ‘Yan Nijeriya tare da iyalansu da gidajensu da Mujami’u da Masallatai da kayan more rayuwa duk sun ruguje a karkashin gwamnatin Buhari.

Kukah ya ce harkokin ilimin kasar ya ruguje tare da rayuwa da makomar ’yaran kasar kamar yadda bangaren siyasa da tattalin arziki da makamashi da al’ummomi da hanyoyin mota da na jiragen kasa suka ruge inda babu abin da ke rayuwa yadda ake bukata da ya wuce cin hanci da rashawa.

Limamin ya ce yau ‘Yan Nijeriya basa iya gane kasar su saboda yadda ta fita daga cikin hayyacin ta sakamakon matsalolin da suka mamaye ta a karkashin gwamnatin Buhari.

Kukah yace lura da irin wadannan dimbin matsalolin da suka addabi Najeriya wasu ‘Yan kasar na tambayar ko masu rike da madafun ikon a basa ji ko gani ko dandanar irin yanayin da jama’ar kasar suka samu kan su ne ko kuma suna nuna halin ko-in-kula ne domin babu abinda ya dame su.

Limamin y ace babban kalubalen dake gaban jam’ar Najeriya ayau itace yadda za’a fara daukar matakin sake dawo da kimar kasar da fatar mutane zasu rayu har zuwa lokacin zaben shekara mai zuwa da kuma sanya ido akan abinda zai biyo baya domin fuskantar matsalolin da suka addabi kasar ta hanyar gina halayen jama’a da kuma son kasa.

Kukah ya bukaci shugabannin addinai da su tashi tsaye cikin gaggawa domin ceto Najeriya daga halin da ta samu kanta, musamman ganin yadda yanzu ake samun miliyoyin mutane a cikin kasar da duniya baki daya dake barin addinin Krista da Musulunci domin zama marasa addinai.

 


No comments