Gwamnan Zamfara a arewacin Najeriya, Bello Matawalle, ya amince da naɗin Alhaji Bashar Isma'il Ari a matsayin Sarkin Burmin Moriki. Wa...
Gwamnan Zamfara a arewacin Najeriya, Bello Matawalle, ya amince da naɗin Alhaji Bashar Isma'il Ari a matsayin Sarkin Burmin Moriki.
Wata wasiƙa daga ofishin Sakataren Gwmanatin Zamfara Kabiru Balarabe ta ce naɗin nasa zai fara aiki daga ranar 10 ga watan Fabarairu.
Mai taimaka wa Gwamna Matawalle kan kafofin yaɗa labarai, Jamilu Iliyasu, ya faɗa cikin wata sanarwa a yau Alhamis cewa an naɗa Bashar Isma'il ne bayan masu naɗin sarki a masarautar sun ba shi maki mafi yawa fiye da sauran abokan takararsa.
Tsohon Sarki Burmin Moriki Alhaji Isma'ila Muhammad Ari II ya rasu ne a ranar 31 ga watan Janairun 2022.
No comments