Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Har Yanzu Babu Labarin Ganin Jaririn Watan Ramadan A Nijeriya

  Sarkin Musulmi, Sultan Alhaji Sa’adu Abubakar Na III Har ya zuwa misalin karfe 7:40 na daren yau Juma’a babu labarin ganin jaririn wata ...

 

Sarkin Musulmi, Sultan Alhaji Sa’adu Abubakar Na III


Har ya zuwa misalin karfe 7:40 na daren yau Juma’a babu labarin ganin jaririn wata Ramadan a fadin Nijeriya.

Kwamitin dake lura da duban wata na Nijeriya a karkashin fadar Mai Martaba Sarkin Musulmi, Sultan Alhaji Sa’adu Abubakar Na III, wato ‘National Moon Sighting Committee - NMSC of NSCIA’ ya wallafa a shafinsa na Facebook da misalin karfe 7:20 na daren yau cewa; har ya zuwa lokacin bai samu labarin ganin wata ba daga garuruwan Bauchi, Gombe, Azare, Misau, Numan, Lagos, Kaduna, Abuja, Bajoga, Nafada, da Maiduguri da sauran su.

Inda suka nemi jin ta bakin masu bibiyarsu dake sauran garuruwa akan cewa ko suna da labarin ganin watan?

Jaridar MADOGARA ta labarto cewa al’ummar Musulmin Nijeriya na ci gaba da sauraren Kwamitin duban watan na Sarkin Musulmi domin fara azumin Ramadana a gobe Asabar ko jinkirtawa zuwa Lahadi idan ba a samu labarin ganin watan ba.

A SAUDIYYAH AN GA JARIRIN WATAN RAMADAN

Hukumar da ke kula da Masallatan Haramai ta bayyana cewa an ga jaririn watan Ramadan a wasu sassan kasar Saudiyya, inda ta bayyana gobe Asabar a matsayin daya ga watan Ramadan a kafatanin kasar.

Rahoton ya ce an samu rahoton ganin watan a wurare daban-daban a fadin kasar.

No comments