Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Harin Boko Haram Ya Kashe Sojoji 11 Da Raunata 19 A Kaduna

Ƴan ta’addan Boko Haram sun kai hari a wani sansanin soji da ke Unguwar Polewire a Birnin Gwari, Jihar Kaduna, inda su ka kashe ...


Ƴan ta’addan Boko Haram sun kai hari a wani sansanin soji da ke Unguwar Polewire a Birnin Gwari, Jihar Kaduna, inda su ka kashe sojoji 11 tare da jikkata wasu 19.

Hakazalika wasu Æ´an kungiyar ‘yan banga uku ma sun rasa rayukansu, yayin da wasu biyu suka samu raunuka yayin harin.

Daily Nigerian Hausa ta jiyo cewa a yakin da aka kwashi tsawon sa’o'i 3 da rabi, wanda aka fara da karfe 4:30 na yamma kuma aka kare da karfe 8 na dare, an kona wasu manyan tankokin yaÆ™i guda uku bayan sun kori sojoji daga wajen.

Majiyoyin tsaro sun ce wurin shi ne babbar hanyar zirga-zirgar ‘yan ta’addar da ke tsallakawa daga Naija zuwa Zamfara.

A cikin rahoton lamarin, wanda wakilinmu ya gani, kayan aikin sojan da aka rasa ko aka lalata sun hada da 1 Legion MRAP; 1 Cobra APC; 1 Styer APC; bindigar injin DSHK; 2 HK 21 bindigogi; 1 GPMG; da bindigogi 14 ƙirar AK47 ; bindigogi masu sarrafa kansu 3; Babura 10, da sauransu.

Ko da yake daga baya an Æ™aro sojoji daga sansanin ‘yan gudun hijira da ke Gwaska da karfe 9:15 na dare, amma babu tabbacin adadin wadanda suka mutu daga bangaren ‘yan ta’addan.

No comments