Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Harin Jirgin Kasa: Gamayyar Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ne Suka Kai Harin -Gwamnati

  Gwamnatin tarayya ta dora alhakin harin Jirgin Kasan Abuja Zuwa Kaduna na kwanakin bayan nan akan hadin gwiwar da ke tsakanin kungiyar Bok...

 


Gwamnatin tarayya ta dora alhakin harin Jirgin Kasan Abuja Zuwa Kaduna na kwanakin bayan nan akan hadin gwiwar da ke tsakanin kungiyar Boko Haram da ‘yan bindiga.

Ministan yada labarai, Lai Mohammed ne ya bayyana hakan ga manema labarai a fadar shugaban kasa bayan taron majalisar zartarwa ta tarayya na mako mako wanda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jagoranta a fadar shugaban kasa a ranar Laraba.

Ya kuma tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa gwamnati na namijin kokari kan shawo gaban lamarin.

Ya ce, “Abin da ke faruwa a yanzu shi ne, akwai wani nau’in hadin kai mara kyau tsakanin ‘yan bindiga da ‘yan Boko Haram.

“Rahotanni na abin da ya faru a harin jirgin kasa na Kaduna ya nuna cewa akwai wani irin hadin gwiwa tsakanin ‘yan bindiga da ‘yan ta’addan Boko Haram da aka fatattaka daga Arewa maso Gabas.

“Zan iya fada muku da kwarin gwiwa cewa Gwamnatin Tarayya tana yin duk me yiwuwa wajen shawo kan lamarin da hada wadanda lamarin ya rutsa dasu da iyalinsu.”

No comments