Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Kiristoci Ke Daukar Nauyin Kashe-kashe A Yankin Kudu Maso Gabas Na Nijeriya –Gwamnan Imo

  Gwamnan Imo, Hope Uzodinma  Gwamnan Jihar Imo dake kudu maso gabashin Nijeriya, Hope Uzodinma ya ce sama da kashi 90 na mutanen dake dau...

 

Gwamnan Imo, Hope Uzodinma 


Gwamnan Jihar Imo dake kudu maso gabashin Nijeriya, Hope Uzodinma ya ce sama da kashi 90 na mutanen dake daukar nauyin kashe kashen da ake samu a Yankin da kuma masu aikata kisan Kiristoci ne.

Uzodinma ya ce abin takaici ne yadda wadannan mutane ke watsi da koyarwar addinin Kirista wajen daukar nauyi da kuma aikata kisan da ya mamaye yankin baki daya.

A sakon sa na bikin Easter Gwamnan ya ce ya roki masu aikata irin wannan laifi da su mayar da wukar su kube domin bai wa jihar damar ci gaba ganin yadda matsalar ta yi matukar illa ga jama’a da kuma al’adun mutanen yankin.

Uzodinma ya ce sau da yawa ya durkusa a kasa yana rokon masu aikata irin wadannan laifuffukan da su daina kashe jama’a ba tare da sun aikata wani laifi ba, yayin da ya roke su da su rungumi zaman lafiya da yafewa juna koda wane laifi aka musu, inda ya ce shima ya nemi gafarar jama’a dangane da laifin da ya aikata musu wajen daukar matakan gwamnatinsa da ba su musu dadi ba.

Gwamnan har wala yau ya kuma bukaci duk wasu masu korafi da su bi matakan shari’a wajen gabatar da korafin su.


No comments