Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Majalisar Pakistan Ta Kori Firaministan Kasar Imran Khan

  Firaministan Pakistan Imran Khan ya rasa matsayinsa a Lahadin nan, bayan da ya sha kaye a zaben majalisar dokokin kasar. An dai sauke Im...

 


Firaministan Pakistan Imran Khan ya rasa matsayinsa a Lahadin nan, bayan da ya sha kaye a zaben majalisar dokokin kasar.

An dai sauke Imran Khan ne, bayan shafe makwanni ana rikicin siyasa a kasar ta Pakistan.

Mukaddashin Kakakin majalisar kasar Sardar Ayaz Sadiq ya ce 'yan majalisa 174 ne suka kada kuri'ar amincewa da kudirin yankan kauna kan jagorancin tsohon Firaminista Imran Khan.

Babu wani Firaminista da ya taba yin cikakken wa'adi a Pakistan, amma Khan shi ne na farko da ya rasa mukaminsa ta hanyar kada kuri'ar rashin gamsuwa da gwamnatinsa.

Ba a dai fayyace lokacin da majalisar Pakistan din za ta zabi sabon Firaministan kasar ba.

No comments