Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Malaman Addini Sun Bukaci A Yi Wa 'Yan Ta'adda Ruwan Bama-Bamai

  Wata tawagar Fastoci dake karkashin wata kungiyar mabiya addinin Kirista ta 'United for Change Association', ta roki gwamnatin Nij...

 


Wata tawagar Fastoci dake karkashin wata kungiyar mabiya addinin Kirista ta 'United for Change Association', ta roki gwamnatin Nijeriya da kuma rundunonin sojin kasar da su kaddamar da gagarumin farmaki kan ‘yan bindigar da suka addabi mutane, ta hanyar yi musu ruwan bama-bamai a cikin dazukan da suke boye a yankunan arewa maso yammaci, jihar Neja da kuma sauran yankin arewa ta tsakiya.

Limaman Cocin sun kuma roki shugaban Nijeriya Muhammad Buhari da ya yi amfani da matsayinsa na Babban Kwamandan daukacin rundunonin tsaron kasar, ya ba da umarnin fara amfani da sabbin jiragen yaki na zamani kirar Super Tucano da gwamnatinsa ta sayo daga Turai, domin murkushe ‘yan ta’addan kowa ma ya huta.

Shugaban kungiyar Fastocin David Adeniran ne ya yi wannan kira, yayin taron nemana labarai da ya gudanar a garin Kaduna, inda ya yi kira da al’ummar Musulmi da ma Kiristoci da su yi amfani da lokacin watan Ramadan wajen yawaita addu’o’in neman samun zaman lafiya.

Karuwar ta’addancin na 'yan bindiga da ake fuskanta a baya bayan nan ne ya sanya gwamnonin wasu daga cikin jihohin arewacin Nijeriya, suka ce a shirye suke su nemo sojin haya domin kare rayuka da kuma dukiyoyin al’umma, matukar dai matsalar ta ci gaba da ta’azzara.

Gwamnan jihar Kaduna Nasir El-rufai, wanda ya zanta da wakilin RFI Hausa, Muhammad Kabiru Yusuf bayan da ya gana da shugaban kasar Muhammadu Buhari a cikin makon da ya gabata, inda ya ce babban abin takaici shi ne yadda jami’an tsaro suka gaza daukar matakin murkushe ‘yan bindigar duk da cewa ana da cikakkun bayanai a game da maboyarsu.

 


No comments