Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Osinbajo Ya Ce Zai Karasa Aikin Da Buhari Bai Kammala Ba Idan Aka Zabe Shi A 2023

  A yau Litinin Mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a zabei 2023. “A yau, ...


 

A yau Litinin Mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a zabei 2023.

“A yau, cikin tawali’u, a hukumance na bayyana aniyara ta tsayawa takarar shugaban kasar Tarayyar Najeriya a Babbar jam’iyyarmu ta APC,” in ji shi a wani faifan bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Sanarwar na sa ta kawo karshen cece-kucen da aka yi na tsawon watanni a kan sha’awarsa a takarar shugaban kasa a 2023 tare da fadada tarin ‘yan takarar kujerar a APC wanda ya hada da Bola Ahmed Tinubu, Rotimi Amaechi, Dave Umahi, Yahaya Bello.

Hakan kuma ya sanya shi yin arangama kai tsaye da tsohon Ubangidansa a jihar Legas, Bola Ahmed Tinubu, wanda ya nuna aniyarsa a farkon shekarar.

A cikin jawabinsa na tsawo minti shida da dakikoki, Fasto Osinbajo ya ce zai jajirce wajen ci gaba da manufofin shugaban kasa Muhammadu Buhari ga kasar.

“Da yardar Allah da yardar jama’a idan aka ba ni dama, to na yi imanin cewa da farko, dole ne mu kammala abin da muka faro, tare da sauya fasalin tsarin tsaro da leken asiri,” in ji shi.


No comments