Grid

GRID_STYLE

Grid

GRID_STYLE

Hover Effects

TRUE

Advertisement

Pages

Labarai:

latest

Advertisement

Ramadan: Ƙungiya Ta Raba Zakkar N2.9m Ga Masallaci, Gidan Marayu Da Sauran Mabuƙata A Kano

Wata Ƙungiya mai Zaman Kanta, mai suna Al-Mubarak Waqf Foundation ta raba Naira Miliyan 2 da su U ɗari 9 a matsayin Zakka ga wani masallac...



Wata Ƙungiya mai Zaman Kanta, mai suna Al-Mubarak Waqf Foundation ta raba Naira Miliyan 2 da su U ɗari 9 a matsayin Zakka ga wani masallaci, gidan marayu da wasu ɗaiɗaikun al'umma a Jihar Kano.

Da ya ke jawabi a yayin rabon zakkar, jami'i a ƙungiyar, Dakta Jamilu Chedi, ya ce an zaɓi waɗanda su ka amfana da zakkar ne duba da dacewar su.

A cewar Chedi, ƙungiyar na da burin ta faɗaɗa wadanda za ta riƙa baiwa zakkar da ga shekara mai zuwa.

Ya ƙara da cewa ƙungiyar, wacce a ka ƙafa ta a 2019, an samar da ita ne domin taimaka wa al'umma da kuma bunƙasa ilimi ga ƴan uwa Musulmi, inda ya ƙara da cewa za ta riƙa tallafa wa wajen ci gaban fasahar zamani da sana'o'i a cikin al'ummar Musulmi.

Dakta Chedi ya kuma baiyana cewa a yanzu haka kungiyar na gina masaallacin Juma'a a unguwar Na'ibawa da ke Jihar Kano, inda ya ƙara da cewa su na kokarin ganin an taimaka wa masu ƙaramin ƙarfi a cikin al'umma don samun zaman lafiya.

Da ya ke jawabi a madadin wadanda su ka amfana da zakkar, Junaidu Ahmad ya nuna jin daɗi da godiya ga ƙungiyar, inda ya tabbatar mata da cewa za su yi amfani da kuɗin da a ka basu ta hanyar da ta dace.


No comments